< Ru’uya ta Yohanna 3 >

1 “Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Sardisu rubuta: ' Wadannan ne kalmomin wanda yake rike da ruhohi bakwai na Allah da taurari bakwai. “Na san abin da ka aikata. Ka yi suna cewa kana raye amma kai mattacce ne.
“And to the messenger of the church in Sardis write: “These things says He who has the seven spirits of God and the seven stars: ‘I know your works, that you have a name that you are alive, yet you are dead.
2 Ka farka ka karfafa abin da ya rage amma ya kusan mutuwa, domin ban sami ayyukanka cikakku a gaban Allahna ba.
Wake up! And strengthen the remaining things that you were about to throw away, for I have not found your works to be fulfilled before my God.
3 Domin haka sai ka tuna, da abubuwan da ka karba kuma kaji. Ka yi biyayya da su, ka kuma tuba. Amma idan baka farka ba, zan zo maka kamar barawo, kuma ba zaka farga da sa'ar da zan zo gaba da kai ba.
So remember how you have received and heard, and hold fast and repent; because if you do not watch, I will come upon you like a thief, and you will not know what hour I will come upon you.
4 Amma akwai sunayen mutane kadan a Sardisu wadanda basu kazantar da tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni sanye da fararen tufafi domin sun cancanta.
“‘But you do have a few names in Sardis who have not defiled their garments, and they will walk with me in white, because they are worthy.
5 Wanda ya yi nasara za a sanya mashi fararen tufafi, kuma ba zan taba share sunansa ba daga Littafin Rai, kuma zan fadi sunansa a gaban Ubana, da kuma gaban mala'ikunsa.
The one who overcomes will thus be clothed in white garments, and I will not erase his name from the Book of Life, and I will confess his name before my Father and before His angels.’
6 Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu ke fadawa ikilisiyoyi.”'”
“He who has an ear let him hear what the Spirit is saying to the churches.
7 Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar cikin Filadelfiya rubuta: kalmomin wanda yake maitsarki ne kuma mai gaskiya - yana rike da mabudin Dauda, yana budewa babu mai rufewa, kuma inda ya rufe ba mai budewa.
“And to the messenger of the church in Philadelphia write: “These things says the Holy, the True, He who has the key of David, who opens and no one can shut it, except He who opens, and no one can open:
8 Na san abin da ka aikata. Duba, na sa budaddiyar kofa a gabanka wanda ba mai iya rufewa. Na san kana da karamin karfi, duk da haka ka yi biyayya da maganata kuma baka yi musun sunana ba.
‘I know your works. Look, I have set before you an open door, that no one is able to shut; because you have a little strength and have kept my Word and have not denied my name.
9 Duba! Wadanda ke na majami'ar Shaidan, wadanda suke cewa su Yahudawa ne; amma maimakon haka karya suke yi. Zan sa su zo su rusuna a kafafunka, kuma za su san cewa ina kaunarka.
See, I am determining that some of the synagogue of Satan, those who claim to be Jews and are not, but are lying—yes, I will cause them to come, and to do obeisance at your feet and to know that I have loved you.
10 Tun da ka jure cikin hakuri ka kiyaye dokoki na, ni ma zan kiyaye ka daga sa'a ta gwaji da zata sauko kan dukan duniya, domin a gwada mazauna duniya.
Because you have kept my command to endure, I also will keep you from the hour of the testing that is about to come upon the whole inhabited earth, to test those who dwell on the earth.
11 Ina zuwa da sauri. Ka rike abin da kake da shi kamkam domin kada wani ya dauke maka rawani.
“‘I am coming swiftly. Hold fast what you have so that no one may take your crown.
12 Zan sa wanda ya yi nasara ya zama ginshiki a haikalin Allahna, kuma ba zai taba fita daga cikin sa ba. Zan rubuta sunan Allahna a kansa, sunan birnin Allahna (sabuwar Urushalima, mai saukowa daga sama daga wurin Allahna), da kuma sabon sunana.
The one who overcomes, I will make him a pillar in the temple of my God, and he will never again go out. And I will write on him the name of my God, the name of my God's city—the new Jerusalem, which comes down out of heaven from my God—and my new name.’
13 Bari wanda yake da kunne ya ji abin da Ruhu ke gayawa ikilisiyoyi.”
“He who has an ear let him hear what the Spirit is saying to the churches.
14 “Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar da ke Lawudikiya rubuta: 'Wadannan sune kalmomin Amin, madogara da mai shaidar gaskiya, mai mulki bisa hallittar Allah.
“And to the messenger of the church in Laodicea write: “These things says the Amen, the faithful and true witness, the Originator of God's creation:
15 Na san abin da ka aikata, ba ka sanyi ko zafi. Naso ko da kana sanyi ko zafi!
‘I know your works, that you are neither cold nor hot. I could wish you were cold or hot.
16 Amma saboda kai tsaka-tsaka ne - ba zafi ba sanyi - na kusa tofar da kai daga bakina.
So then, since you are lukewarm, and neither hot nor cold, I am about to vomit you out of my mouth.
17 Domin ka ce, “Ni mai arziki ne, na mallaki kadarori da yawa, ba na bukatar komai.” Amma ba ka sani ba kana cike da takaici ne, abin tausayi, matalauci, makaho kuma tsirara kake.
Because you say, “I am rich, even become wealthy, and have need of nothing,” and do not realize that you are the most wretched—yes, the most pitiable and poor and blind and naked—
18 Saurari shawara ta: Ka sayi zinariya a wuri na wadda aka goge da wuta domin ka zama mai arziki, domin ka suturta kanka da fararen tufafi masu kyalli domin kada ka nuna kunyar tsiraicin ka, da mai domin ka shafa wa idanunka ka sami gani.
I counsel you to buy gold from me, refined by fire, so that you may become rich; and white garments, so that you may be clothed, and your nakedness not be shamefully exposed; and anoint your eyes with eye salve, so that you may see.
19 Ina horar da duk wanda nake kauna, ina kuma koya masu yadda za su yi rayuwa. Saboda haka, ka himmatu ka tuba.
As many as I love I rebuke and discipline; so be zealous and repent!
20 Duba, ina tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa. Idan wani ya ji muryata ya bude kofar, zan shigo cikin gidansa, in ci tare da shi, shi kuma tare da ni.
“‘Now then, I stand at the door and knock. If anyone should hear my voice and open the door, I really will come in to him and eat with him, and he with me.
21 Wanda ya ci nasara, zan bashi dama ya zauna tare da ni bisa kursiyina, kamar yadda nima na ci nasara kuma na zauna da Ubana a kan kursiyinsa.
To the one who overcomes I will grant to sit with me on my throne, just as I overcame and sat down with my Father on His throne.’
22 Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu yake fadawa wa ikilisiyoyi.”
“He who has an ear let him hear what the Spirit is saying to the churches.”

< Ru’uya ta Yohanna 3 >