< Ru’uya ta Yohanna 3 >

1 “Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Sardisu rubuta: ' Wadannan ne kalmomin wanda yake rike da ruhohi bakwai na Allah da taurari bakwai. “Na san abin da ka aikata. Ka yi suna cewa kana raye amma kai mattacce ne.
“And to the Angel of the Church of Sardis write: Thus says he who has the seven spirits of God and the seven stars: I know your works, that you have a name which is alive, but you are dead.
2 Ka farka ka karfafa abin da ya rage amma ya kusan mutuwa, domin ban sami ayyukanka cikakku a gaban Allahna ba.
Be vigilant, and confirm the things that remain, lest they soon die out. For I do not find your works to be full in the sight of my God.
3 Domin haka sai ka tuna, da abubuwan da ka karba kuma kaji. Ka yi biyayya da su, ka kuma tuba. Amma idan baka farka ba, zan zo maka kamar barawo, kuma ba zaka farga da sa'ar da zan zo gaba da kai ba.
Therefore, keep in mind the way that you have received and heard, and then observe it and repent. But if you will not be vigilant, I will come to you like a thief, and you will not know at what hour I will come to you.
4 Amma akwai sunayen mutane kadan a Sardisu wadanda basu kazantar da tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni sanye da fararen tufafi domin sun cancanta.
But you have a few names in Sardis who have not defiled their garments. And these shall walk with me in white, because they are worthy.
5 Wanda ya yi nasara za a sanya mashi fararen tufafi, kuma ba zan taba share sunansa ba daga Littafin Rai, kuma zan fadi sunansa a gaban Ubana, da kuma gaban mala'ikunsa.
Whoever prevails, so shall he be clothed in white vestments. And I will not delete his name from the Book of Life. And I will confess his name in the presence of my Father and in the presence of his Angels.
6 Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu ke fadawa ikilisiyoyi.”'”
Whoever has an ear, let him hear what the Spirit says to the Churches.
7 Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar cikin Filadelfiya rubuta: kalmomin wanda yake maitsarki ne kuma mai gaskiya - yana rike da mabudin Dauda, yana budewa babu mai rufewa, kuma inda ya rufe ba mai budewa.
And to the Angel of the Church of Philadelphia write: Thus says the Holy One, the True One, he who holds the key of David. He opens and no one closes. He closes and no one opens.
8 Na san abin da ka aikata. Duba, na sa budaddiyar kofa a gabanka wanda ba mai iya rufewa. Na san kana da karamin karfi, duk da haka ka yi biyayya da maganata kuma baka yi musun sunana ba.
I know your works. Behold, I have set an open door before you, which no one is able to close. For you have little power, and you have observed my word, and you have not denied my name.
9 Duba! Wadanda ke na majami'ar Shaidan, wadanda suke cewa su Yahudawa ne; amma maimakon haka karya suke yi. Zan sa su zo su rusuna a kafafunka, kuma za su san cewa ina kaunarka.
Behold, I will take from the synagogue of Satan those who declare themselves to be Jews and are not, for they are lying. Behold, I will cause them to approach and to reverence before your feet. And they shall know that I have loved you.
10 Tun da ka jure cikin hakuri ka kiyaye dokoki na, ni ma zan kiyaye ka daga sa'a ta gwaji da zata sauko kan dukan duniya, domin a gwada mazauna duniya.
Since you have kept the word of my patient endurance, I also will keep you from the hour of temptation, which shall overcome the whole world in order to test those living upon the earth.
11 Ina zuwa da sauri. Ka rike abin da kake da shi kamkam domin kada wani ya dauke maka rawani.
Behold, I am approaching quickly. Hold on to what you have, so that no one may take your crown.
12 Zan sa wanda ya yi nasara ya zama ginshiki a haikalin Allahna, kuma ba zai taba fita daga cikin sa ba. Zan rubuta sunan Allahna a kansa, sunan birnin Allahna (sabuwar Urushalima, mai saukowa daga sama daga wurin Allahna), da kuma sabon sunana.
Whoever prevails, I will set him as a column in the temple of my God, and he shall not depart from it anymore. And I will write upon him the name of my God, and the name of the city of my God, the new Jerusalem that descends out of heaven from my God, and my new name.
13 Bari wanda yake da kunne ya ji abin da Ruhu ke gayawa ikilisiyoyi.”
Whoever has an ear, let him hear what the Spirit says to the Churches.
14 “Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar da ke Lawudikiya rubuta: 'Wadannan sune kalmomin Amin, madogara da mai shaidar gaskiya, mai mulki bisa hallittar Allah.
And to the Angel of the Church of Laodicea write: Thus says the Amen, the faithful and true Witness, who is the Beginning of the creation of God:
15 Na san abin da ka aikata, ba ka sanyi ko zafi. Naso ko da kana sanyi ko zafi!
I know your works: that you are neither cold, nor hot. I wish that you were either cold or hot.
16 Amma saboda kai tsaka-tsaka ne - ba zafi ba sanyi - na kusa tofar da kai daga bakina.
But because you are lukewarm and are neither cold nor hot, I will begin to vomit you out of my mouth.
17 Domin ka ce, “Ni mai arziki ne, na mallaki kadarori da yawa, ba na bukatar komai.” Amma ba ka sani ba kana cike da takaici ne, abin tausayi, matalauci, makaho kuma tsirara kake.
For you declare, ‘I am wealthy, and I have been enriched further, and I have need of nothing.’ And you do not know that you are wretched, and miserable, and poor, and blind, and naked.
18 Saurari shawara ta: Ka sayi zinariya a wuri na wadda aka goge da wuta domin ka zama mai arziki, domin ka suturta kanka da fararen tufafi masu kyalli domin kada ka nuna kunyar tsiraicin ka, da mai domin ka shafa wa idanunka ka sami gani.
I urge you to buy from me gold, tested by fire, so that you may be enriched and may be clothed in white vestments, and so that the shame of your nakedness may disappear. And anoint your eyes with an eye salve, so that you may see.
19 Ina horar da duk wanda nake kauna, ina kuma koya masu yadda za su yi rayuwa. Saboda haka, ka himmatu ka tuba.
Those whom I love, I rebuke and chastise. Therefore, be zealous and do penance.
20 Duba, ina tsaye a bakin kofa ina kwankwasawa. Idan wani ya ji muryata ya bude kofar, zan shigo cikin gidansa, in ci tare da shi, shi kuma tare da ni.
Behold, I stand at the door and knock. If anyone will hear my voice and will open the door to me, I will enter to him, and I will dine with him, and he with me.
21 Wanda ya ci nasara, zan bashi dama ya zauna tare da ni bisa kursiyina, kamar yadda nima na ci nasara kuma na zauna da Ubana a kan kursiyinsa.
Whoever prevails, I will grant to him to sit with me on my throne, just as I also have overcome and have sat down with my Father on his throne.
22 Bari wanda yake da kunne ya saurari abin da Ruhu yake fadawa wa ikilisiyoyi.”
Whoever has an ear, let him hear what the Spirit says to the Churches.”

< Ru’uya ta Yohanna 3 >