< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala'ika ya nuna mani kogin ruwan rai, ruwa mai tsabta. Yana fitowa daga cikin kursiyin Allah da na Dan-Rago
The angel showed me the river of water [that causes people who drink from it] to live [forever]. The water was sparkling and clear like crystal. The river was flowing out from the throne where God and the [one who is like a] lamb [were sitting].
2 ta tsakiyar titin birnin. A kowanne gefen kogin akwai itacen rai, mai ba da 'ya'ya iri goma sha biyu, kowanne wata. Ganyayen itacen kuma domin warkar da al'ummai ne.
It flowed down through the middle of the [main] street of the city. On each side of the river were trees [bearing fruit that causes people who eat it] to live forever. [The trees] bear twelve [crops] (OR, twelve [kinds]) of fruit; [they] produce one crop each month. The [people of the] nations [MTY] [use] the leaves of these trees [as medicine] in order that they may feel stronger
3 Babu sauran la'ana nan gaba. Kursiyin Allah da na Dan Rago za su kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa bauta.
There will never be [anyone or anything there that God] will be [under God’s] curse. The throne of God and the [one who is like a] lamb will be in the city. And God’s servants will worship him there.
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
They will see him face-to-face, and his name will be [written] {[he] will [write] his name} on their foreheads.
5 Babu sauran dare; ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba gama Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su yi mulki har abada abadin. (aiōn )
There will never again be night. [God’s servants] will not need the light of a lamp or the light of the sun, because the Lord God will shine his light upon them. And they will rule forever. (aiōn )
6 Mala'ika ya ce mani, “Wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya. Ubangiji, Allah na ruhohin annabawa, ya aiki mala'ikansa ya nuna wa bayinsa abin da lallai zai faru ba da dadewa ba”.
The angel said to me: “These words that [God has revealed to you] are true, and he will certainly do what he has promised to do. The Lord God who ([inspires] the prophets/tells the prophets what to say) sent his angel to show the people who serve him the events that must happen soon.”
7 “Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba! Mai albarka ne wanda ya yi biyayya da kalmomin littafin nan.”
[Jesus says to all his people], “Listen [to] this! I am coming soon; [God will abundantly] bless everyone who obeys what [has been commanded] in this book.”
8 Ni, Yahaya, nine na ji na kuma ga wadannan abubuwa. Sa'adda na ji na gan su, sai na fadi gaban kafaffun mala'ikan da ya nuna mani wadannan abubuwa domin in yi masa sujada.
I, John, am the one who heard and saw [in a vision] these things [that I have written down]. When I had heard and seen [them], I immediately knelt down at the feet of the angel who was showing them to me, in order to worship him.
9 Ya ce mani, “Kada ka yi haka! Ni abokin bauta ne tare da kai, tare da 'yan'uwanka annabawa, da wadanda ke biyayya da kalmomin littafin nan. Yi sujada ga Allah!”
But he said to me, “Do not [worship me] I am [just] your fellow servant! I am also the fellow servant of your fellow believers who are (the prophets/the ones who tell messages that come directly from God), and I am a fellow servant of those who obey what has been commanded in this book. [Instead], worship God!”
10 Ya ce mani, “Kada ka rufe kalmomin anabcin littafin nan, gama lokaci ya kusa.
He also said to me, “Do not keep secret the message about what [God] has foretold in this book, because it is almost time [MTY] for him to [what he has promised to do in this message].
11 Wanda yake mara adalci, bari ya cigaba da yin rashin adalci. Wanda yake mai kazanta bari ya cigaba da kazantar da kansa. Wanda yake mai adalci bari ya cigaba da yin adalci. Wanda yake mai-tsarki, bari yaci gaba da tsarki.”
[Since that time is near, if] those who act in an evil manner [want to] continue to act that way [IRO], [that is up to them. God will soon] ([pay them back/punish them]) [for that. If] those who are vile [want to] continue to be vile [IRO], [that is up to them. God will soon] ([pay them back/punish them]) [for that]. Those who are [acting] righteously should continue to act righteously. And those who are holy should continue to be holy.”
12 “Duba! Ina zuwa ba da dadewa ba. Sakamakona na tare da ni, zan saka wa kowa gwargwadon aikin da ya yi.
[Jesus says this to everyone]: “Listen! I am coming soon! And I will pay back everyone according to what each one has done, by [punishing or] rewarding them.
13 Nine Alpha da Omega, farko da karshe, mafarin abu da karshensa.
I [am] the one who began all things [MET] and the one who will cause all things to end [MET]. I existed before [all things existed] and I will exist at the end [of all things] [DOU].
14 Masu albarka ne wadanda suka wanke rigunansu domin su sami izini su ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta kofofinsa.
[God] is very pleased with the people who wash their robes, [making themselves spiritually clean] [MET], because they will be able to [eat the fruit of] [MTY] the tree [that enables people] to live [forever], and because they will [be able] to enter the gates into the [holy] city.
15 A waje akwai karnuka, masu sihiri, masu bautar gumaka, fasikai, masu kisan kai, da duk wanda yake kaunar aikata rashin gaskiya.
[People who are unholy] will not be allowed to enter the city. They include people who practice sorcery, people who sin sexually, murderers, idol worshipers, and everyone who enjoys telling lies and are continual liars. [They can never enter that city].”
16 Ni, Yesu na aiko mala'ikana ya shaida maku wadannan abubuwa saboda ikilisiyoyi. Nine tushe da zuriyar Dauda, tauraron asubahi mai-haske.”
“I, Jesus, sent my angel in order that he might tell you who are in the congregations [that all] these things [that have been said are true]. I am the descendant of [King] David [whom the prophets promised would come] [MET]. I am the [one who is like] the bright morning star [MET], the one [that Moses promised would come].”
17 Ruhu da Amarya suka ce, “Zo!” Bari wanda ya ji ya ce, “Zo!” Kowanne mai jin kishi, da kowanne mai bukatar ta, bari ya sami ruwan rai kyauta.
[God’s] Spirit and [his people, who are like] [MET] the bride [of Christ], say [to each one who desires to believe], “Come!” Whoever hears [this] should also say [to each one who desires to believe], “Come!” [Spiritually thirsty people should come] [MET]! Everyone who desires the water [that enables people to] live [forever] should take it as a free gift!
18 Ina shaida wa duk mai jin kalmomin anabcin wannan littafi: Idan wani ya kara a kansu, Allah zai kara masa annoban da ke rubuce a cikin littafin.
“I, [Jesus, solemnly] warn everyone who hears what [I] have foretold in this book: If anyone adds anything to this message, God will cause him to experience the plagues that are {that [I] have} described in this book.
19 Idan wani ya rage daga kalmomin wannan littafin anabci, Allah zai rage rabonsa daga cikin itacen rai daga cikin birni mai-tsarki, wadanda aka rubuta cikin wannan littafi.
If anyone omits any of the message about what [I] have foretold in this book, God will take away that person’s right [to eat fruit from] [MTY] the tree [that enables people] to live [forever]. He [will also take away] that person’s right [to enter] God’s city. [Both these things] are described {[I] have described [both these things]} in this book.”
20 Shi wanda ya shaida wadannan abubuwa ya ce, “I! Ina zuwa ba da dadewa ba.” Amin! Zo, Ubangiji Yesu!
[Jesus], who says that [all] the things written here are true, says, “Certainly I am coming soon!” [I, John, reply], “(May it be so!/Amen!) Lord Jesus, come!”
21 Alherin Ubangiji Yesu ya kasance tare da kowanne dayanku. Amin.
[I pray that our] Lord Jesus [will continue to] act kindly to all [of you who are God’s people]. (Amen!/May it be so!)