< Ru’uya ta Yohanna 21 >
1 Sai na ga sabuwar sama da sabuwar duniya, domin sama ta fari da duniya ta fari sun shude, ba kuma teku.
Depois, vi um novo céu e uma nova terra surgirem. O primeiro céu e a primeira terra desapareceram, e o mar não existia mais.
2 Na ga birni mai tsarki, sabuwar Urushalima, wadda ta sauko kasa daga sama wurin Allah, shiryayya kamar amaryar da aka yi wa ado domin mijinta.
Eu vi a cidade santa, a Nova Jerusalém, que descia do céu. Ela vinha da parte de Deus e estava preparada e enfeitada como uma noiva que fica bonita para o seu marido.
3 Na ji babbar murya daga kursiyinta na cewa, “Duba! Mazaunin Allah yana tare da 'yan adam, zai zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kuma da kansa zai kasance tare da su ya kuma zama Allahnsu.
Eu ouvi uma voz bem alta, que vinha do trono, dizer: “Agora, a casa de Deus está com os homens, e ele irá viver com eles. Eles serão o povo de Deus. O próprio Deus estará com eles como o seu Deus.
4 Zai share dukan hawaye daga idanunsu, kuma babu sauran mutuwa, ko bakinciki, ko kuka, ko azaba. Abubuwan da sun shude.
Ele enxugará as lágrimas de seus olhos e nunca mais haverá morte. Também não mais haverá tristeza, choro ou dor, pois o mundo antigo não existe mais.”
5 Shi wanda yake zaune a kan kursiyin ya ce, “Duba! Na maida kome ya zama sabo.” Ya ce, “Ka rubuta wannan domin wadannan kalmomi amintattu ne da gaskiya”.
Aquele que está sentado no trono disse: “Eu estou fazendo tudo novo!” Ele me disse: “Escreva isto, pois estas palavras são dignas de confiança e são verdadeiras.”
6 Ya ce mani, “Wadannan abubuwan an gama! Ni ne Alpha da Omega, farko da karshe. Ga mai jin kishi, zan bashi kyauta daga mabulbular ruwan rai.
E, então, ele continuou a dizer: “Tudo está feito! Eu sou o Alfa e o Ômega, o Começo e o Fim. Para todos os que têm sede, eu darei água, de graça, da fonte da água da vida.
7 Wanda ya ci nasara, zai gaji wadannan abubuwa, ni kuma zan zama Allahnsa, shi kuma ya zama da na.
Aqueles que forem vitoriosos herdarão todas essas coisas, e eu serei o seu Deus e eles serão os meus filhos.
8 Amma ga matsorata, da marasa bangaskiya, da masu kazanta, da masu kisan kai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da dukan makaryata, mazaunin su zai kasance cikin tafki mai ci da farar wuta. Mutuwa ta biyu kenan.” (Limnē Pyr )
Mas qualquer um que se mostre covarde, que não tenha fé em mim, que cometa atos repugnantes, que seja assassino, que seja imoral, que pratique feitiçaria, que adore ídolos, ou que minta, já tem o seu lugar designado. Ele será jogado no lago que queima com fogo e enxofre. Esta é a segunda morte.” (Limnē Pyr )
9 Daya daga cikin mala'ikun bakwai ya zo wurina, wanda yake dauke da tasoshi bakwai cike da annobai bakwai na karshe, yace, “Zo nan. Zan nuna maka amarya, matar Dan Rago”.
Um dos sete anjos com as sete taças que continham as sete últimas pragas veio e falou comigo. Ele me disse: “Venha comigo! Eu irei lhe mostrar a noiva, a esposa do Cordeiro.”
10 Sai ya dauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsawo ya nuna mani birni mai-tsarki, Urushalima, tana saukowa daga cikin sama daga wurin Allah.
E ele me levou, pelo Espírito, para cima de uma montanha muito alta. Lá, ele me mostrou a cidade santa, Jerusalém, que descia do céu, vinda da parte de Deus
11 Urushalima tana da daukakar Allah, shekinta yana kama da dutse mai tamani, sai kace dutsen yasfa, garau kamar karau.
e que brilhava com a glória da presença de Deus. A luz da cidade brilhava como a de uma pedra preciosa, como uma pedra de jaspe, clara e brilhante.
12 Tana da babban garu mai tsawo, da kofofi goma sha biyu, da mala'iku goma sha biyu a kofofin. Akan kofofin an rubuta sunayen kabilu sha biyu na 'ya'yan Isra'ila.
Os muros que a cercavam eram altos e sólidos, com doze portões guardados por doze anjos. Nos portões estavam escritos os nomes das doze tribos de Israel.
13 A gabas akwai kofofi uku, a arewa kofofi uku, a kudu kofofi uku, da kuma yamma kofofi uku.
Havia três portões a leste, três ao norte, três ao sul e três a oeste.
14 Garun birnin yana da harsashin gini goma sha biyu, a bisansu akwai sunaye goma sha biyu na manzanni goma sha biyu na Dan Rago.
A muralha da cidade tinha doze fundamentos e, em cada um deles, estava escrito o nome de um dos doze apóstolos do Cordeiro.
15 Shi wanda yayi magana dani yana da sandan awo na zinariya domin ya auna birnin, da kofofinsa, da garunsa.
O anjo que conversava comigo segurava uma vara de ouro para medir a cidade, seus portões e seus muros.
16 Birnin; da tsawonsa da fadinsa iri daya ne. Ya gwada birnin da sandar awo, mil dubu sha biyu a tsaye (fadinsa, da tsawonsa, da tsayinsa duka daya ne)
O formato da cidade era quadrado, pois o seu comprimento era semelhante a sua largura. Ele mediu a cidade com a vara, e viu que media aproximadamente dois mil e quatrocentos quilômetros. O comprimento, a largura e a altura eram semelhantes.
17 Ya kuma gwada garunsa, kamu 144, bisa ga gwajin 'yan adam (wanda shine ma'aunin mala'ika).
Ele mediu a muralha, que tinha mais de sessenta metros de espessura, conforme as medidas humanas que o anjo estava usando.
18 An gina garun da Yasfa birnin kuma da sahihiyar zinariya, mai kama da madubi mai kyalli.
Os muros eram feitos de jaspe. A cidade era feita de ouro puro e era clara como o vidro.
19 An kawata harsashin garun da kowanne irin dutse mai tamani. Na fari yasfa, na biyu saffir, na uku agat, na hudu emerald,
Os fundamentos da muralha da cidade eram decorados com todos os tipos de pedras preciosas. O primeiro fundamento era de jaspe; o segundo, de safira; o terceiro, de ágata; o quarto, de esmeralda;
20 na biyar Onis, na shida sardiyus, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha daya yakinta, na sha biyu kuma ametis.
o quinto, de sardônica; o sexto, de sárdio; o sétimo, de crisólito; o oitavo, de berilo; o nono, de topázio; o décimo, de crisópraso; o décimo primeiro, de jacinto e o décimo segundo, de ametista.
21 Kofofi goma sha biyu lu'u-lu'ai ne goma sha biyu; kowacce daya a cikin kofofin daga lu'u-lu'u daya aka yi shi. Titunan birnin kuwa zinariya ce sahihiya, sai kace madubi garau.
Os doze portões eram feitos de pérola, e cada um deles era feito de uma única pérola. A rua principal era feita de ouro puro, clara como o vidro.
22 Ban ga haikali a cikin birnin ba, gama Ubangiji Allah Mai iko duka da Dan Ragon su ne haikalinsa.
Eu não vi um templo por lá, porque o Senhor Deus, o Todo-Poderoso, e o Cordeiro eram o templo da cidade.
23 Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi gama daukakar Allah ta haskaka shi, kuma fitilarsa Dan Rago ne.
A cidade não precisa do sol nem da lua para a iluminar, pois a glória de Deus dá toda a luz que ela precisa, e o Cordeiro é a sua lâmpada.
24 Al'ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin. Sarakunan duniya kuma za su kawo daukakarsu cikinsa.
As nações irão andar pela sua luz, e os reis da terra trarão as suas riquezas para a cidade.
25 Kofofinsu kuma ba za a rufe su da rana ba, babu dare kuma a can.
Seus portões nunca ficarão fechados durante o dia e nela não haverá noite.
26 Za su kawo daukaka da darajar al'ummai a cikinsa,
As nações trarão para a cidade os seus tributos e as suas riquezas.
27 babu wani abu mai kazanta da zai taba shiga cikinsa. Ko wanda yake aikata abin kunya da karya, sai wadanda an rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Dan Rago kadai.
Nada que seja impuro entrará na cidade, assim como também ninguém que adore ídolos ou que minta. Apenas aqueles que têm os seus nomes escritos no Livro da Vida do Cordeiro poderão passar pelos seus portões.