< Ru’uya ta Yohanna 18 >

1 Bayan wadannan abubuwa sai na ga wani mala'ika yana saukowa daga sama. Yana da babban iko sosai, duniya kuwa ta haskaka da daukakarsa.
Après cela, je vis descendre du ciel un autre ange qui avait une grande puissance, et la terre était illuminée de sa gloire,
2 Ya yi kira da kakkarfar murya cewa, “Ta fadi, Babila mai girma ta fadi! Ta zama mazaunin aljannu, da matattarar kowanne kazamin ruhu da kuma mazaunin kowanne kazami da kyamataccen tsuntsu.
et il cria d'une voix formidable: «Elle est tombée, elle est tombée, la grande Babylone, elle est devenue une demeure de démons, un refuge d'Esprits impurs, un refuge d'oiseaux immondes et détestés,
3 Gama dukan al'ummai sun sha ruwan innabin fasikancinta. Sarakunan duniya sun aikata fasikanci da ita. Attajiran duniya sun arzuta da ikon rayuwar annashuwarta.”
parce que toutes les nations ont bu du vin de feu de sa fornication, et que les rois de la terre ont forniqué avec elle, et que les marchands de la terre se sont enrichis de son opulence.»
4 Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fito daga cikinta, mutanena, domin kada kuyi zunubi irin na ta, domin kuma kada bala'inta ya auko maku.
Et j'entendis une autre voix qui venait du ciel et disait: «Sortez d'elle, ô mon peuple, pour ne pas vous rendre complices de ses péchés et pour n'être pas atteints par les plaies qui vont la frapper.
5 Zunubanta sun taru sun yi tsayi har sama. Allah kuma ya tuna da miyagun ayyukanta.
Ses péchés se sont accumulés jusqu'au ciel, et Dieu s'est souvenu de ses iniquités.
6 Ku saka mata gwargwadon yadda ta saka wa wadansu, ku biya ta ninki biyu na abin da ta yi; a cikin kokon da ta dama, ku dama mata ninki biyu.
Faites-lui ce qu'elle a fait aux autres; payez-la au double de ses oeuvres, versez-lui à boire le double de la coupe qu'elle a versée aux autres.
7 Kamar yadda ta daukaka kanta ta yi ta annashuwa, ku wahalsheta da azaba da bakin ciki haka. Domin ta ce a zuciyarta, 'Ina zaune kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taba yin makoki ba,'
Autant elle a eu de gloire et d'opulence, autant donnez-lui de tourment et d'affliction. «Je suis assise en reine, dit-elle en son coeur, je ne suis pas' veuve, et je ne connaîtrai jamais le deuil.»
8 Saboda haka a rana daya bala'inta zai auko mata; mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta za ta kona ta kurmus, domin Ubangiji Allah mai iko ne, kuma shine mai hukuntata.”
Voilà pourquoi toutes ses plaies viendront en un même jour, mort, et désolation, et famine, et destruction par le feu, car puissant est le Seigneur Dieu qui l'a jugée.»
9 Sarakunan duniya da suka yi fasikanci, har suka baude tare da ita, za su yi kuka da kururuwa domin ta sa'adda suka ga hayakin kunarta.
Et l'on verra pleurer et se lamenter sur elle les rois de la terre qui ont forniqué avec elle et ont eu leur part de son opulence. A la vue de la fumée de son embrasement
10 Za su tsaya can nesa suna tsoron azabarta, suna cewa, “Kaito, kaiton babban birni, Babila, birni mai iko! Domin cikin sa'a guda hukuncinta ya zo.”
et se tenant à distance par crainte de ses tourments: «Malheur! malheur! diront-ils, Quoi! la grande ville! Babylone! la puissante ville! en une heure est venu ton jugement!»
11 Manyan 'yan kasuwan duniya za su yi kuka da bakin ciki dominta, da shike ba wanda ke sayan kayanta kuma -
Et les marchands de la terre pleureront et se désoleront sur elle, car personne n'achète plus leurs marchandises:
12 kayan zinariya, azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'u-lu'u, da lilin mai laushi, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jar alharini da itacen kamshi iri iri, da kayan da aka sassaka da itace mai tsada, da na tagulla, da na bakin karfe, da na dutse mai sheki,
marchandises d'or et d'argent, et pierres précieuses, et perles, et fin lin, et pourpre, et soie, et écarlate, et bois de thuia, et objets en ivoire, et objets en bois précieux, et en bronze, et en fer, et en marbre;
13 da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur da lubban, da ruwan innabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawakai, da kekunan doki, da bayi, da rayukan 'yan adam.
et cinname, et amome, et parfums, et huiles aromatiques, et encens, et vin, et huile, et fleur de farine, et froment, et boeufs, et brebis, et chevaux, et chars, et corps et âmes d'hommes.
14 Amfanin da kika kwallafa rai da duk karfinki sun fice daga gareki. Duk annashuwarki da darajarki sun bace, ba za a kara samunsu ba kuma.
Et toute cette moisson de choses que convoitait ton âme s'en est allée loin de toi, et toutes ces choses brillantes et magnifiques sont perdues pour toi, et tu ne le trouveras plus jamais.
15 Manyan 'yan kasuwa na wadannan kaya da suka azurta ta wurinta, za su tsaya can nesa da ita, sabili da tsoron azabarta, kuka da kururuwar bakin ciki.
Les marchands de toutes ces choses qui se sont enrichis par elles, se tenant à distance par crainte de ses tourments, pleurant
16 Za su ce, “Kaito, kaito ga babban birni da take sanye da lilin mai laushi da tufafi masu jar garura da kuma jan alharini, da ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsu masu daraja da lu'u-lu'u!
et se désolant: «Malheur! malheur! diront-ils, Quoi! la grande ville vêtue d'écarlate, et de pourpre, et de fin lin, parée d'or et de pierres précieuses et de perles!
17 A cikin sa'a guda duk dukiyan nan ta lallace. Kowanne matukin jirgin ruwa, da fasinjoji, da masu tuki da duk wadanda suke samun biyan bukatun rayuwarsu daga ruwa, suka tsaya can nesa.
En une heure ont péri tant de richesses!» Et les pilotes et les marins qui venaient vers elle, et les matelots, et tous ceux qui trafiquent de la mer, s'arrêtant à distance,
18 Suka yi kuka sa'anda suka ga hayakin kunarta. Suka ce, “Wanne birni ne ya yi kama da babban birnin?”
se répandent en cris à la vue de la fumée de son incendie: «Quelle ville, disent-ils, égalait la grande ville?»
19 Suka watsa kura a kawunansu, suka yi kuka da karfi, da kururuwa da bakin ciki, “Kaito, kaiton babban birnin nan inda duk masu jiragen ruwa suka azurta daga dukiyarta. Domin a sa'a guda an hallakar da ita.”
et ils jettent de la poussière sur leur tête et se répandent en cris, en pleurs, et en lamentations. «Malheur! malheur! disent-ils, grande ville qui enrichissait de ses trésors tous ceux qui avaient des vaisseaux sur la mer; en une seule heure elle a été changée en désert!»
20 “Ku yi murna a kanta, sama, ku masu ba da gaskiya, manzanni, da annabawa, domin Allah ya kawo hukuncinku a kanta!”
Réjouis-toi de sa ruine, ô ciel; et vous, les saints, et les apôtres, et les prophètes, réjouissez-vous, car Dieu a vengé votre cause sur elle.»
21 Wani kakkarfan mala'ika ya dauki wani dutse mai kama da dutsen nika, ya jefa shi cikin teku yana cewa, “Ta wannan hanya, Babila, babban birnin, za a jefar da ita kasa da karfi, ba za a kara ganinsa ba.
Et un ange d'une force extraordinaire prit une pierre grosse comme une meule et la lança dans la mer en disant: «C'est avec cette violence que sera précipitée Babylone, la grande ville, et on ne la retrouvera plus jamais.
22 Muryar masu kidar molaye, mawaka, masu busa sarewa, da na masu busa algaita, ba za a kara ji a cikinta ba. Babu wani mai kowanne irin sana'a da za a samu a cikinta. Ba za a kara jin karar nika a cikinta ba.
Et la voix des joueurs de harpe, et des musiciens, et des joueurs de flûte et de trompette ne résonnera plus dans tes murs; ni artisan, ni métier ne se trouvera désormais chez toi;
23 Hasken fitila ba za ya kara haskakawa a cikin ki ba. Ba za a kara jin muryoyin ango da na amarya a cikinki ba, domin attajiranki sune 'ya'yan masu mulki a duniya, kuma ta wurin sihirinki kika yaudari al'ummai.
le bruit de la meule ne s'y fera point entendre; la lumière de la lampe n'y brillera plus jamais; et la voix du fiancé et celle de la fiancée ne s'y feront plus entendre; car tes marchands étaient les grands de la terre, et ce sont tes enchantements qui ont égaré toutes les nations,
24 A cikinta aka sami jinin annabawa da na masu ba da gaskiya, da jinin duk wadanda aka kashe a duniya.”
et c'est là qu'on a trouvé le sang des prophètes, et des saints, et de tous ceux qui ont été égorgés sur la terre.

< Ru’uya ta Yohanna 18 >