< Ru’uya ta Yohanna 16 >

1 Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, ''Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya.”
And I heard a loud voice from the sanctuary saying to the seven angels, “Go, pour out the bowls of God's fury on the earth.”
2 Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.
So off went the first one and poured out his bowl on the earth, and a foul and malignant ulcer appeared in the people who had the mark of the beast and those who worshiped his image.
3 Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'
Then the second angel poured out his bowl on the sea, and it turned into blood, like a dead person's; so every living soul in the sea died.
4 Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini.
Then the third angel poured out his bowl on the rivers and the springs of water, and they turned into blood.
5 Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, ''Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa.
And I heard the angel of the waters saying: “How just You are! The One who is and who was, the holy One, because You have judged these things.
6 Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su.
Because they shed the blood of saints and prophets, and You have given them blood to drink. They deserve it!”
7 Na ji bagadi ya amsa, ''I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci.''
And I heard one from the altar saying: “Yes, O Lord God, the Almighty! Your judgings are true and just!”
8 Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta.
Then the fourth angel poured out his bowl on the sun, and it was granted to him to burn the people with fire.
9 Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.
So the people were burned with severe burns, and they blasphemed the name of God, who has authority over these plagues. And they did not repent to give Him glory.
10 Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi.
Then the fifth angel poured out his bowl on the throne of the Beast, and his kingdom was plunged into darkness; so they gnawed their tongues because of the pain.
11 Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.
And they blasphemed the God of heaven because of their pains, and because of their ulcers; yet they did not repent of their deeds.
12 Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas.
Then the sixth angel poured out his bowl on the great river Euphrates, and its water was dried up, so that the way for the kings from the sun's rising might be prepared.
13 Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi.
And I saw three unclean spirits, like frogs, coming out of the mouth of the dragon, out of the mouth of the Beast, and out of the mouth of the false prophet.
14 Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.
For they are spirits of demons, performing signs, which go out to the kings of the whole inhabited earth, to gather them to the battle of that great day of God Almighty.
15 (''Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.”)
(“Watch out, I am coming like a thief. Blessed is the one who watches and guards his clothes, so that he not walk about naked and they see his shame.”)
16 Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.
So he gathered them to the place called in Hebrew, Armagedon.
17 Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, ''An gama!''
Then the seventh angel poured out his bowl into the air, and a great voice came out of the sanctuary of heaven, from the Throne, saying, “It is done!”
18 Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke.
and there were lightnings and thunders and noises. And there was a tremendous earthquake, a terribly severe earthquake such as had not occurred since mankind existed on the earth.
19 Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.
So the great city was divided into three parts, and the cities of the nations fell. And Babylon the great was remembered before God, to give her the cup of the wine of the fury of His wrath.
20 Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba.
And every island fled, and mountains were not found.
21 Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.
And huge hailstones, weighing about a talent, fell out of the sky on the people; and the people blasphemed God on account of the plague of the hail, because its plague was exceedingly severe.

< Ru’uya ta Yohanna 16 >