< Ru’uya ta Yohanna 13 >
1 Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku. Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo.
And he took up a position upon the sands of the sea-shore. Then I saw a Wild Beast coming up out of the sea, and he had ten horns and seven heads. On his horns were ten kingly crowns, and inscribed on his heads were names full of blasphemy.
2 Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.
The Wild Beast which I saw resembled a leopard, and had feet like the feet of a bear, and his mouth was like the mouth of a lion; and it was to the Dragon that he owed his power and his throne and his wide dominion.
3 Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban.
I saw that one of his heads seemed to have been mortally wounded; but his mortal wound was healed, and the whole world was amazed and followed him.
4 Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, “Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?”
And they offered worship to the Dragon, because it was to him that the Wild Beast owed his dominion; and they also offered worship to the Wild Beast, and said, "Who is there like him? And who is able to engage in battle with him?"
5 Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu.
And there was given him a mouth full of boastful and blasphemous words; and liberty of action was granted him for forty-two months.
6 Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.
And he opened his mouth to utter blasphemies against God, to speak evil of His name and of His dwelling-place--that is to say, of those who dwell in Heaven.
7 Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma.
And permission was given him to make war upon God's people and conquer them; and power was given him over every tribe, people, language and nation.
8 Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.
And all the inhabitants of the earth will be found to be worshipping him: every one whose name is not recorded in the Book of Life--the Book of the Lamb who has been offered in sacrifice ever since the creation of the world.
9 Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi.
Let all who have ears give heed.
10 Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.
If any one is eager to lead others into captivity, he must himself go into captivity. If any one is bent on killing with the sword, he must himself be killed by the sword. Here is an opportunity for endurance, and for the exercise of faith, on the part of God's people.
11 Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji.
Then I saw another Wild Beast, coming up out of the earth. He had two horns like those of a lamb, but he spoke like a dragon.
12 Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.
And the authority of the first Wild Beast--the whole of that authority--he exercises in his presence, and he causes the earth and its inhabitants to worship the first Wild Beast, whose mortal wound had been healed.
13 Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane.
He also works great miracles, so as even to make fire come down from Heaven to earth in the presence of human beings.
14 Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.
And his power of leading astray the inhabitants of the earth is due to the marvels which he has been permitted to work in the presence of the Wild Beast. And he told the inhabitants of the earth to erect a statue to the Wild Beast who had received the sword-stroke and yet had recovered.
15 Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban.
And power was granted him to give breath to the statue of the Wild Beast, so that the statue of the Wild Beast could even speak and cause all who refuse to worship it to be put to death.
16 Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi.
And he causes all, small and great, rich and poor, free men and slaves, to have stamped upon them a mark on their right hands or on their foreheads,
17 Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.
in order that no one should be allowed to buy or sell unless he had the mark--either the name of the Wild Beast or the number which his name represents.
18 Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.
Here is scope for ingenuity. Let people of shrewd intelligence calculate the number of the Wild Beast; for it indicates a certain man, and his number is 666.