< Ru’uya ta Yohanna 13 >

1 Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku. Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo.
And I sawe a best rise out of the see havinge vii. heddes and x. hornes and apon hys hornes x. crownes and apon his heed the name of blasphemy.
2 Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.
And the beast which I sawe was lyke a catt of the mountayne and his fete were as the fete of a bear and his mouth as the mouthe of a lyon. And the dragon gave him his power and his seate and grett auctorite:
3 Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban.
and I sawe one of his heedes as it were wouded to deth and his dedly woude was healed. And all the worlde wondred at the beast
4 Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, “Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?”
and they worshipped ye drago which gave power vnto the beest and they worshipped the beest sayinge: who is lyke vnto the beast? who is able to warre with him?
5 Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu.
And ther was a mouth geve vnto him that spake great thinges and blasphemies and power was geve vnto him to do xlii. Monethes
6 Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.
And he opened his mowth vnto blasphemy agaynst God to blaspheme hys name and his tabernacle and them that dwell in heven.
7 Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma.
And it was geven vnto him to make warre with the saynctes and to overcome them. And power was geven him over all kynred tonge and nacion:
8 Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.
and all that dwell apon the erth worshipt him: whose names are not written in the boke of lyfe of the lambe which was kylled from the begynnynge of the worlde.
9 Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi.
Yf eny man have an eare lett him heare.
10 Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.
He that leadeth into captivite shall goo into captivite: he that kylleth with a swearde must be kylled with a swearde. Heare is the pacience and the fayth of the saynctes.
11 Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji.
And I behelde another best commynge vp oute of the erth and he had two hornes like a lambe and he spake as dyd the dragon.
12 Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.
And he dyd all that the fyrste beest coulde do in his presence and he caused the erth and them which dwell therin to worshippe the fyrst beest whose dedly woude was healed.
13 Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane.
And he dyd grett wonders so that he made fyre come doune from heven in the syght of men.
14 Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.
And deceaved them that dwelt on the erth by the meanes of those signes which he had power to doo in the sight of the beest sayinge to the that dwelt on the erth: that they shuld make an ymage vnto the beest which had the woude of a swearde and dyd lyve.
15 Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban.
And he had power to geve a sprete vnto the ymage of the beest and that the ymage of the beest shuld speake and shuld cause that as many as wolde not worshyppe the ymage of the beest shuld be kylled.
16 Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi.
And he made all bothe smale and grett ryche and poore fre and bond to receave a marke in their right hondes or in their forheddes.
17 Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.
And that no ma myght by or sell save he that had the marke or the name of the beest other the nombre of his name.
18 Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.
Here is wisdome. Let him that hath wytt count the nombre of the beest. For it is the nombre of a man and his nombre is sixe hondred threscore and sixe.

< Ru’uya ta Yohanna 13 >