< Ru’uya ta Yohanna 13 >

1 Sai diragon ya tsaya a kan yashi, a gaban teku. Sai na ga wani dabba yana fitowa daga teku. Yana da kahonni goma da kawuna bakwai. A kan kahonninsa akwai kambi goma, a kan kowanne kansa akwai suna na sabo.
And I stood on the sand of the sea, and I saw a beast coming up out of the sea, having seven heads and ten horns, and ten crowns on its horns, and on its heads names of slander,
2 Wannan dabban da na gani yana kama da damisa, kafafunsa kuma kamar na beyar, bakinsa kuma kamar na zaki. Wannan diragon ya ba shi karfinsa, da kursiyinsa da ikonsa mai girma na sarauta.
and the beast that I saw was like to a leopard, and its feet as of a bear, and its mouth as the mouth of a lion, and the dragon gave to it his power, and his throne, and great authority.
3 Daya daga cikin kawunan dabban ya yi kamar an kashe shi, amma rauninsa mai tsanani ya warke. Sai dukan duniya ta yi mamaki a yayin da suke bin dabban.
And I saw one of its heads as slain to death, and its deadly wound was healed, and all the earth wondered after the beast,
4 Su ma suka yi wa diragon sujada, domin ya ba dabban ikonsa. Suka yi wa dabban sujada suna ta cewa, “Wanene kamar dabban? Wa kuma zai iya yin fada da shi?”
and they worshiped the dragon who gave authority to the beast, and they worshiped the beast, saying, “Who [is] like to the beast? Who is able to war with it?”
5 Aka ba dabban baki da zai iya fadin kalmomin fahariya da sabo. Ya sami izini na zartar da iko har wata arba'in da biyu.
And there was given to it a mouth speaking great things, and slanders, and there was given to it authority to make war forty-two months,
6 Sai dabban ya bude bakinsa yana maganganun sabo ga Allah: yana sabon sunansa, da mazauninsa, da kuma wadanda ke zaune a sama.
and it opened its mouth for slander toward God, to slander His Name, and of His dwelling place, and of those who dwell in Heaven,
7 Aka yarje wa dabbar ya yi yaki da masu bi ya kuma yi nasara da su. An kuma ba shi iko bisa kowacce kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma.
and there was given to it to make war with the holy ones, and to overcome them, and there was given to it authority over every tribe, and tongue, and nation.
8 Dukan wadanda ke zaune a duniya za su yi masa sujada, dukan wadanda tun hallitar duniya ba a rubuta sunayensu a littafin rai na Dan Rago ba, wanda aka yanka.
And all who are dwelling on the earth will worship him, whose names have not been written in the Scroll of Life of the Lamb slain from the foundation of the world;
9 Idan wani yana da kunne, bari ya ji. Duk wanda za a dauke shi zuwa bauta, ga bauta zai tafi.
if anyone has an ear—let him hear:
10 Duk wanda za a kashe da takobi, da takobi za a kashe shi. Wannan kira ne na dauriya, hakuri da bangaskiya ga wadanda suke da tsarki.
if anyone [goes] into captivity, into captivity he goes; if anyone is to be killed with sword, it is necessary of him by sword to be killed; here is the endurance and the faith of the holy ones.
11 Sai na ga wani dabban na fitowa daga cikin kasa. Yana da kahonni biyu kamar na dan rago, ya kuma yi magana kamar maciji.
And I saw another beast coming up out of the earth, and it had two horns like a lamb, and it was speaking as a dragon,
12 Ya zartar da dukan ikon dabban na farko a gabansa, ya kuma sa duniya da duk mazaunanta su yi wa dabban nan na farko sujada, wanda aka warkar masa da rauni mai kamar na ajali.
and all the authority of the first beast does it do before it, and it makes the earth and those dwelling in it that they will worship the first beast, whose deadly wound was healed,
13 Ya yi manyan al'ajibai. Har ya sa wuta ta sauko kasa daga sama a gaban mutane.
and it does great signs, that fire also it may make to come down from the sky to the earth before men,
14 Ta wurin alamu da aka yarje masa ya yi, ya yaudari mazaunan duniya. Ya ce masu su yi wata siffa don girmama dabban da yake da raunin takobi, amma duk da haka ya rayu.
and it leads astray those dwelling on the earth, because of the signs that were given it to do before the beast, saying to those dwelling on the earth to make an image to the beast that has the wound of the sword and lived,
15 Aka yarje masa ya ba da numfashi ga siffar dabban domin siffar ta yi magana, ta kuma sa a kashe duk wadanda suka ki yin sujada ga dabban.
and there was given to it to give a spirit to the image of the beast, that also the image of the beast may speak, and it may cause as many as will not worship the image of the beast, that they may be killed.
16 Ya kuma tilasta kowa, kanana da manya, mawadata da matalauta, masu yanci da bayi, su karbi alama a hannun dama ko kuma a goshi.
And it makes all, the small, and the great, and the rich, and the poor, and the freemen, and the servants, that it may give to them a mark on their right hand or on their foreheads,
17 Ba shi yiwuwa wani ya saya ko ya sayar sai dai yana da alamar dabban, wato lambar nan da ke wakiltar sunansa.
and that no one may be able to buy, or to sell, except he who is having the mark, or the name of the beast, or the number of his name.
18 Wannan na bukatar hikima. Idan wani yana da hikima, sai ya kididdige lambar dabban nan. Gama lambar ta mutum ce. Lambarta itace 666.
Here is the wisdom! He who is having the understanding, let him count the number of the beast, for it is the number of a man, and its number: six hundred sixty-six.

< Ru’uya ta Yohanna 13 >