< Ru’uya ta Yohanna 12 >

1 Aka ga wata babbar alama a sama: wata mace ta yi lullubi da rana, kuma wata na karkashin kafafunta; rawanin taurari goma sha biyu na bisa kanta.
Then a great sign appeared in heaven: a woman clothed with the sun, with the moon under her feet and a crown of twelve stars on her head.
2 Tana da ciki, tana kuma kuka don zafin nakuda - a cikin azabar haihuwa.
She was with child and cried out in the pain and agony of giving birth.
3 Sai aka ga wata alama cikin sama: Duba! Akwai wani katon jan maciji mai kawuna bakwai da kahonni goma, sai kuma ga kambi guda bakwai bisa kawunansa.
Then another sign appeared in heaven: behold, a great fiery red dragon with seven heads and ten horns, and seven diadems on his heads.
4 Wutsiyarsa ta share daya bisa uku na taurari a sama ta zubo su kasa. Diragon nan ya tsaya a gaban matar da ta kusan haihuwa, domin lokacin da ta haihu ya lankwame yaronta.
His tail swept down a third of the stars of heaven and hurled them to the earth. Then the dragon stood in front of the woman who was about to give birth, so that when she gave birth he might devour her child.
5 Sai ta haifi da, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al'ummai da sandar karfe. Aka fizge yaron ta zuwa ga Allah da kursiyinsa,
She gave birth to a son, a male child, who is to rule all the nations with a rod of iron, but her child was caught up to God and to his throne.
6 matar kuwa ta gudu zuwa jeji inda Allah ya shirya mata domin a iya lura da ita kwanaki 1, 260.
And the woman fled into the wilderness, where God had a place prepared for her to be nourished for one thousand two hundred sixty days.
7 A lokacin sai yaki ya tashi a sama. Mika'ilu da mala'ikunsa suka yi yaki da diragon, sai diragon da nasa mala'iku suka yake su su ma.
Then war broke out in heaven; Michael and his angels fought against the dragon. And the dragon fought back, along with his angels.
8 Amma diragon ba shi da isashen karfin da zai ci nasara. Don haka, shi da mala'ikunsa ba su kara samun wuri a sama ba.
But he did not prevail, and there was no longer any place found for him in heaven.
9 Sai aka jefa katon diragon nan tare da mala'ikunsa kasa, wato tsohon macijin nan da ake kira Iblis ko Shaidan wanda ke yaudarar dukan duniya.
The great dragon was thrown down, the old serpent, who is called the devil and Satan, the deceiver of the whole world. He was thrown down to the earth, and his angels were thrown down with him.
10 Sai na ji wata murya mai kara a sama: “Yanzu ceto ya zo, karfi, da mulkin Allahnmu, da iko na Almasihunsa. Gama an jefar da mai sarar 'yan'uwanmu a kasa - shi da yake sarar su a gaban Allah dare da rana.
Then I heard a loud voice in heaven saying, “The salvation, power, and kingdom of our God, and the authority of his Christ, have now come. For the accuser of our brothers has been thrown down, he who accuses them day and night before our God.
11 Suka ci nasara da shi ta wurin jinin Dan Ragon da kuma shaidar maganarsu, gama ba su kaunaci ransu ba, har ga mutuwa.
They overcame him by the blood of the Lamb and by the word of their testimony; they did not love their lives so as to shy away from death.
12 Don haka, yi farinciki, ya ku sammai da duk mazauna da ke cikinsu. Amma kaito ga duniya da teku saboda iblis ya sauko gare ku. Yana cike da mummunan fushi, domin ya san lokacin sa ya rage kadan.
Therefore rejoice, O heavens and you who dwell in them! But woe to the earth and the sea! For the devil has come down to you with great wrath, because he knows that his time is short.”
13 Da diragon ya ga an jefar da shi kasa, sai ya fafari matar nan da ta haifi da namiji.
When the dragon saw that he had been thrown down to the earth, he pursued the woman who had given birth to the male child.
14 Amma aka ba matar nan fukafukai biyu na babbar gaggafa domin ta gudu zuwa inda aka shirya mata a jeji. A wannan wuri ne za a lura da ita na dan lokaci, da lokatai, da rabin lokaci - a lokacin da babu macijin.
But the woman was given two wings like those of a great eagle so that she could fly away from the presence of the serpent to her place in the wilderness, to be nourished there for a time, times, and half a time.
15 Macijin ya kwararo ruwa daga bakin sa kamar kogi, don ya kawo ambaliyar da zai kwashe ta.
Then out of his mouth the serpent spewed water like a river after the woman, to sweep her away with a flood.
16 Amma kasa ta taimaki matar. Kasa ta bude bakinta ta hadiye kogin da diragon ya kwararo daga bakinsa.
But the earth helped the woman by opening its mouth and swallowing the river that the dragon had spewed out of his mouth.
17 Sai diragon ya fusata da matar, sai ya tafi ya yi yaki da sauran zuriyarta, wadanda suka yi biyayya da umarnan Allah suna kuma rike da shaida game da Yesu.
So the dragon was angry with the woman and went off to wage war against the rest of her offspring, those who keep the commandments of God and hold to the testimony of Jesus.

< Ru’uya ta Yohanna 12 >