< Ru’uya ta Yohanna 12 >

1 Aka ga wata babbar alama a sama: wata mace ta yi lullubi da rana, kuma wata na karkashin kafafunta; rawanin taurari goma sha biyu na bisa kanta.
AND a great sign was seen in heaven; a woman clothed with the sun, and the moon beneath her feet, and upon her head a crown of twelve stars.
2 Tana da ciki, tana kuma kuka don zafin nakuda - a cikin azabar haihuwa.
And having in her womb, she cried, and was in travail, and was pained to give birth.
3 Sai aka ga wata alama cikin sama: Duba! Akwai wani katon jan maciji mai kawuna bakwai da kahonni goma, sai kuma ga kambi guda bakwai bisa kawunansa.
And I saw another sign in heaven; and behold a great dragon of fire, which had seven heads and ten horns, and upon his heads seven diadems.
4 Wutsiyarsa ta share daya bisa uku na taurari a sama ta zubo su kasa. Diragon nan ya tsaya a gaban matar da ta kusan haihuwa, domin lokacin da ta haihu ya lankwame yaronta.
And his tail drew the third of the stars of heaven, and cast them to the earth. And the dragon stood before the woman when she was about to give birth, that when she had given birth he might devour her son.
5 Sai ta haifi da, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al'ummai da sandar karfe. Aka fizge yaron ta zuwa ga Allah da kursiyinsa,
And she gave birth to a male child, who is to rule all nations with a rod of iron; and her son was rapt unto Aloha and unto his throne.
6 matar kuwa ta gudu zuwa jeji inda Allah ya shirya mata domin a iya lura da ita kwanaki 1, 260.
And the woman fled into the desert, where she had a place prepared of Aloha, that there they might nourish her, DAYS A THOUSAND AND TWO HUNDRED AND SIXTY.
7 A lokacin sai yaki ya tashi a sama. Mika'ilu da mala'ikunsa suka yi yaki da diragon, sai diragon da nasa mala'iku suka yake su su ma.
And there was war in heaven. And Mikoel and his angels to fight with the dragon; and the dragon and his angels warred.
8 Amma diragon ba shi da isashen karfin da zai ci nasara. Don haka, shi da mala'ikunsa ba su kara samun wuri a sama ba.
And they could not prevail, and their place was found no more in heaven.
9 Sai aka jefa katon diragon nan tare da mala'ikunsa kasa, wato tsohon macijin nan da ake kira Iblis ko Shaidan wanda ke yaudarar dukan duniya.
And the great dragon was cast down, the old serpent, who is called the Deceiver, and the Adversary, which seduceth the whole habitable world. And he was cast upon the earth, and his angels with him were cast.
10 Sai na ji wata murya mai kara a sama: “Yanzu ceto ya zo, karfi, da mulkin Allahnmu, da iko na Almasihunsa. Gama an jefar da mai sarar 'yan'uwanmu a kasa - shi da yake sarar su a gaban Allah dare da rana.
And I heard a great voice in heaven saying, Now is there salvation and strength, And the kingdom of our God, And the power of his Meshiha; Because the accuser of our brethren is cast down, Who accused them before Aloha day and night.
11 Suka ci nasara da shi ta wurin jinin Dan Ragon da kuma shaidar maganarsu, gama ba su kaunaci ransu ba, har ga mutuwa.
And they overcame him by the blood of the Lamb, And by the word of his testimony. But they loved not their lives unto death.
12 Don haka, yi farinciki, ya ku sammai da duk mazauna da ke cikinsu. Amma kaito ga duniya da teku saboda iblis ya sauko gare ku. Yana cike da mummunan fushi, domin ya san lokacin sa ya rage kadan.
Wherefore let the heavens be glad, And those who dwell in them. Woe to the earth and to the sea! Because the deceiver hath gone down to you, Having great indignation, Knowing that little time is to him.
13 Da diragon ya ga an jefar da shi kasa, sai ya fafari matar nan da ta haifi da namiji.
And when the dragon saw that he was cast down upon the earth, he pursued the woman which gave birth to the son.
14 Amma aka ba matar nan fukafukai biyu na babbar gaggafa domin ta gudu zuwa inda aka shirya mata a jeji. A wannan wuri ne za a lura da ita na dan lokaci, da lokatai, da rabin lokaci - a lokacin da babu macijin.
And there were given to the woman two wings of a great eagle, that she might fly into the desert unto her place, where she was to be nourished A TIME, AND TIMES, AND THE DIVIDING OF A TIME, from the face of the serpent.
15 Macijin ya kwararo ruwa daga bakin sa kamar kogi, don ya kawo ambaliyar da zai kwashe ta.
And the serpent cast forth from his mouth after the woman waters like a river, as that she might be carried off by the river which he would make.
16 Amma kasa ta taimaki matar. Kasa ta bude bakinta ta hadiye kogin da diragon ya kwararo daga bakinsa.
And the earth succoured the woman, and the earth opened her mouth, and swallowed the river which the dragon had cast forth from his mouth.
17 Sai diragon ya fusata da matar, sai ya tafi ya yi yaki da sauran zuriyarta, wadanda suka yi biyayya da umarnan Allah suna kuma rike da shaida game da Yesu.
And the dragon raged against the woman, and went to make war with those of the rest of her seed which kept the commandments of Aloha, and had the testimony of Jeshu.

< Ru’uya ta Yohanna 12 >