< Ru’uya ta Yohanna 12 >

1 Aka ga wata babbar alama a sama: wata mace ta yi lullubi da rana, kuma wata na karkashin kafafunta; rawanin taurari goma sha biyu na bisa kanta.
And a great sign appeared in heaven, a woman clothed with the sun; and the moon was under her feet, and on her head was a crown of twelve stars;
2 Tana da ciki, tana kuma kuka don zafin nakuda - a cikin azabar haihuwa.
and, being with child, she cried out in travail, and in the pains of delivery.
3 Sai aka ga wata alama cikin sama: Duba! Akwai wani katon jan maciji mai kawuna bakwai da kahonni goma, sai kuma ga kambi guda bakwai bisa kawunansa.
And there appeared another sign in heaven; and behold, a great dragon, fiery-red, that had seven heads, and ten horns: and on his heads seven diadems.
4 Wutsiyarsa ta share daya bisa uku na taurari a sama ta zubo su kasa. Diragon nan ya tsaya a gaban matar da ta kusan haihuwa, domin lokacin da ta haihu ya lankwame yaronta.
And his tail drew along the third part of the stars of heaven, and did cast them to the earth. And the dragon stood before the woman who was about to bring forth, that, when she had brought forth, he might devour her child.
5 Sai ta haifi da, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al'ummai da sandar karfe. Aka fizge yaron ta zuwa ga Allah da kursiyinsa,
And she brought forth a male child, that was to rule all nations with a rod of iron; and her child was caught away to God, even to his throne.
6 matar kuwa ta gudu zuwa jeji inda Allah ya shirya mata domin a iya lura da ita kwanaki 1, 260.
And the woman fled into the wilderness, where she has a place prepared by God, that they should feed her there for a thousand two hundred and sixty days.
7 A lokacin sai yaki ya tashi a sama. Mika'ilu da mala'ikunsa suka yi yaki da diragon, sai diragon da nasa mala'iku suka yake su su ma.
And there was war in heaven; Michael and his angels fought with the dragon; and the dragon and his angels fought,
8 Amma diragon ba shi da isashen karfin da zai ci nasara. Don haka, shi da mala'ikunsa ba su kara samun wuri a sama ba.
and prevailed not: nor was their place found any more in heaven.
9 Sai aka jefa katon diragon nan tare da mala'ikunsa kasa, wato tsohon macijin nan da ake kira Iblis ko Shaidan wanda ke yaudarar dukan duniya.
And the great dragon, that old serpent, called the Devil, and Satan, who deceives the whole world, was cast into the earth, and his angels were cast out with him.
10 Sai na ji wata murya mai kara a sama: “Yanzu ceto ya zo, karfi, da mulkin Allahnmu, da iko na Almasihunsa. Gama an jefar da mai sarar 'yan'uwanmu a kasa - shi da yake sarar su a gaban Allah dare da rana.
And I heard a great voice in heaven, saying: Now has come the salvation, and the power, and the kingdom of our God, and the authority of his Christ: for the accuser of our brethren, he that accused them before our God day and night, is cast down.
11 Suka ci nasara da shi ta wurin jinin Dan Ragon da kuma shaidar maganarsu, gama ba su kaunaci ransu ba, har ga mutuwa.
And they overcame him by the blood of the Lamb, and by the word of their testimony; and they loved not their lives even to death.
12 Don haka, yi farinciki, ya ku sammai da duk mazauna da ke cikinsu. Amma kaito ga duniya da teku saboda iblis ya sauko gare ku. Yana cike da mummunan fushi, domin ya san lokacin sa ya rage kadan.
Therefore, rejoice you heavens, and you that dwell in them. Alas for the land and for the sea! for the devil has come down to you with great anger, because he knows that he has but a short time.
13 Da diragon ya ga an jefar da shi kasa, sai ya fafari matar nan da ta haifi da namiji.
And when the dragon saw that he was cast into the earth, he persecuted the woman that brought forth the male child.
14 Amma aka ba matar nan fukafukai biyu na babbar gaggafa domin ta gudu zuwa inda aka shirya mata a jeji. A wannan wuri ne za a lura da ita na dan lokaci, da lokatai, da rabin lokaci - a lokacin da babu macijin.
And two wings of a great eagle were given to the woman, that she might fly into the wilderness into her place, where she is nourished for a time, and times, and half a time, away from the presence of the serpent.
15 Macijin ya kwararo ruwa daga bakin sa kamar kogi, don ya kawo ambaliyar da zai kwashe ta.
And the serpent threw out of his mouth water like a river, after the woman, that he might cause her to be carried away by the river.
16 Amma kasa ta taimaki matar. Kasa ta bude bakinta ta hadiye kogin da diragon ya kwararo daga bakinsa.
And the earth helped the woman; and the earth opened her mouth, and swallowed up the river that the dragon threw out of his mouth.
17 Sai diragon ya fusata da matar, sai ya tafi ya yi yaki da sauran zuriyarta, wadanda suka yi biyayya da umarnan Allah suna kuma rike da shaida game da Yesu.
And the dragon was angry with the woman, and went away to make war with the rest of her children, that keep the commandments of God, and that hold the testimony of Jesus.

< Ru’uya ta Yohanna 12 >