< Mattiyu 8 >

1 Da Yesu ya sauko daga dutsen, sai taro masu yawa suka bi shi.
Як же зійшов з гори, багато народу йшло слїдом за Ним.
2 Sai wani kuturu ya zo gunsa ya yi masa sujada, ya ce, “Ubangiji, in dai ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
Коли се приступив прокажений і вклонивсь Йому, кажучи: Господи, коли хочеш, то зможеш очистити мене,
3 Yesu ya mika hannunsa ya taba shi, ya ce, “Na yarda, ka tsarkaka.” Nan da nan aka tsarkake shi daga kuturtarsa.
І простяг Ісус руку, й приторкнувсь до него, й рече: Хочу, очистись. І зараз очистилась проказа його.
4 Yesu ya ce masa, 'Ka tabbata, ba ka gaya wa kowa komai ba. Sai dai ka je ka nuna kan ka ga firist, ka kuma bayar da baiko da Musa ya umarta domin shaida garesu?
І рече до него Ісус: Гледи ж, не кажи нїкому, а йди та покажись священикові, й принеси дар, який повелїв Мойсей на сьвідкуваннє їм.
5 Da Yesu ya shiga kafarnahum, sai wani hafsa ya zo gunsa ya roke shi,
А як увійшов Ісус у Капернаум, приступив до Него сотник, благаючи Його,
6 Ya ce, Ubangiji, bawana na kwance shanyayye a gida, yana shan azaba kwarai.”
й говорячи: Господи, слуга мій лежить дома розслаблений, і тяжко мучить ся.
7 Yesu ya ce masa, “Zan zo in warkar da shi.”
І рече до него Ісус: Я пійду та сцїлю його.
8 Sai hafsan, ya ce, “Ubangiji, ban isa har ka zo gida na ba, amma sai ka yi magana kawai, bawana kuwa zai warke.
Озвав же ся сотник і сказав: Господи, не заслужив я того, щоб Ти ввійшов під мою стелю; а промов одно слово, то й одужає слуга мій.
9 Domin ni ma ina karkashin ikon wani ne, ina kuma da sojoji a karkashina, sai in ce wa wannan, 'je ka,' sai ya je, wani kuma in ce masa, 'zo,' sai ya zo, in ce wa bawa na, 'yi abu kaza,' sai ya yi,”
Бо сам я чоловік під властю, і маю воїни під собою; і скажу сьому: Йди, то й іде; а другому: Прийди, то й прийде, а слузї моєму: Роби те, то й робить.
10 Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki, har ya ce wa mabiyansa, “Gaskiya, ina gaya maku, ko a cikin isra'ila ban taba samun bangaskiya mai karfi irin wannan ba.
Почувши се Ісус, дивував ся, і рече до тих, що йшли слїдом за Ним: Істино кажу вам: Навіть в Ізраїлї не знайшов я такої віри.
11 Na gaya maku, da yawa za su zo daga gabas da yamma, su zauna cin abinci tare da Ibrahim da Ishaku, da Yakubu a cikin mulkin sama.
І кажу вам: Що многі прийдуть од сходу й заходу, та й сядуть з Авраамом, з Ісааком і з Яковом у царстві небесному,
12 Amma 'ya'yan mulkin kuwa sai a jefa su cikin matsanancin duhu. Can za su yi kuka da cizon hakora.”
а сини царства будуть повикидані у темряву надвірню: там буде плач і скриготаннє зубів.
13 Yesu ya ce wa hafsan, “Je ka! Bari ya zamar maka gwargwadon bangaskiyar da ka yi,” A daidai wannan sa'a bawansa ya warke.
І рече Ісус до сотника: Йди, і, як вірував єси, станеть ся тобі. І одужав слуга його тієї самої години.
14 Da Yesu ya shiga gidan Btrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance da zazzabi.
І прийшов Ісус до Петрової господи, та й побачив, що теща його лежить у пропасниці.
15 Yesu ya taba hannunta, zazzabin ya sake ta, ta kuma tashi ta fara yi masa hidima.
І приторкнувсь до руки її, й покинула пропасниця її, й вставши вона, послуговала їм.
16 Da maraice ya yi, sai mutanen suka kakkawo wa Yesu masu aljanu da yawa. Da magana kawai ya fitar da aljanun, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
Як же настав вечір, приведено до Него багато біснуватих; і повиганяв Він біси словом, і сцїлив усїх недужих;
17 Ta haka kuwa maganar annabi Ishaya ta samu cika cewa, “Shi da kansa ya debe rashin lafiyar mu, ya dauke cututtukan mu.”
щоб справдилось, що сказав Ісаїя пророк, глаголючи: Узяв Він на себе недуги наші, й понїс болещі наші.
18 Sa'adda Yesu ya ga taro masu yawa kewaye da shi, sai ya ba da umarni su tafi su koma wancan hayi na tekun Galili.
Як же побачив Ісус великий натовп кругом себе, то звелїв плисти на той бік.
19 Sai wani marubuci ya zo ya ce masa, “Malam, zan bi ka duk inda za ka je.”
І приступивши один письменник, каже до Него: Учителю, пійду слідом за Тобою, куди б Ти нї пійшов.
20 Yesu ya ce masa, “Yanyawa suna da ramukansu, tsuntsayen sama kuma da shekunan su, amma Dan mutum ba shi da wurin da zai kwanta.”
Ісус же рече до него: Лисицї мають нори, й птаство небесне гнізда; Синові ж чоловічому нїде й голови прихилити.
21 Wani cikin almajiran ya ce masa, “Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne mahaifina.”
Другий же ученик Його каже до Него: Господи, дозволь менї перш пійти поховати батька мого.
22 Amma Yesu ya ce masa, “Bari matattu su binne matattunsu.”
Ісус ж рече до него: Йди слїдом за мною; нехай мертві ховають мерці свої.
23 Da Yesu ya shiga jirgi, almajiransa suka bi shi.
І, як увійшов у човен, поввіходили слїдом за Ним ученики Його.
24 Sai ga wata babbar iska ta taso a tekun, har rakuman ruwa suka fara shan kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
Аж ось схопилась велика хуртовина на морі, така що филя заливала човна; Він же спав.
25 Sai almajiran sa suka je suka tashe shi, suka ce, “Ubangiji, ka cece mu, za mu hallaka!”
І, приступивши ученики Його, розбудили Його, кажучи: Господи, спаси нас: погибаємо.
26 Yesu ya ce masu, “Don me kuka firgita haka, ya ku masu karancin bangaskiya?” Sa'annan ya tashi, ya tsauta wa iskar da tekun. Sai wurin gaba daya ya yi tsit.
І рече до них: Чого ви злякались, маловірні? Тодї встав, і погрозив вітрам та морю; і настала велика тиша.
27 Mutanen suka yi al'ajibi, suka ce, “Wanne irin mutum ne wannan, wanda har iska da teku ma suke masa biyayya?”.
Люде ж дивувались, говорячи: Хто се такий, що й вітри й море слухають Його!
28 Da Yesu ya zo daga wancan hayin a kasar Garasinawa, mutane biyu masu al'janu suka fito suka same shi. Suna fitowa daga makabarta kuma suna da fada sosai, har ma ba mai iya bin ta wannan hanya.
І як переплив на той бік у Гергесинську землю, зустріло Його два біснуватих, що вийшли з гробів, вельми злющі, так що ніхто не важив ся ходити дорогою тією.
29 Sai suka kwala ihu suka ce, “Ina ruwanka da mu, kai dan Allah? Ka zo nan ne ka yi mana azaba tun kafin lokaci ya yi?”
І ось, закричали, говорячи: Що нам і Тобі, Ісусе, Сину Божий? чи на те прийшов єси сюди, щоб нас заздалегідь мучити?
30 To akwai wani garken aladu masu yawa na kiwo, babu nisa da su.
Оддалеки ж од них пас ся великий гурт свиней.
31 Sai al'janun suka roki Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
А біси благали Його, кажучи: Коли нас виженеш, то дозволь нам увійти в гурт свинячий.
32 “Yesu ya ce masu, “To, ku je.” Sai aljanun suka fita, suka shiga cikin aladun. Sai kuwa duk garken suka rugungunta ta gangaren, suka fada cikin tekun, suka hallaka a ruwa.
І рече до них: Ійдїть. І, вийшовши вони, увійшли в стадо свиняче - коли се увесь гурт свинячий кинувсь із кручі в море, та й потонув у водї
33 Mutanen masu kiwon aladun suka gudu, suka shiga gari, suka yi ta ba da labarin komai da komai, musamman abin da ya faru da masu al'janun.
А пастухи повтікали й, прибігши в город, росказали про все й про біснуватих.
34 Sai duk jama'ar gari suka fito su sami Yesu. Da suka gan shi, suka roke shi ya bar kasarsu.
І ось увесь город вийшов назустріч Ісусові, а, побачивши Його благали, щоб вийшов геть із гряниць їх.

< Mattiyu 8 >