< Mattiyu 6 >
1 Ku yi hankali kada ku yi ayyukan adalcinku gaban mutane domin su ganku, idan kun yi haka, ba za ku sami sakamako a wurin Ubanku da yake sama ba.
Vogter eder at i ikke øve eders Retfærdighed for Menneskene for at beskues af dem; ellers have I ikke Løn hos eders Fader, som er Himlene.
2 Saboda haka, in za ku yi sadaka, kada ku busa kaho yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma akan tituna domin mutane su yabesu. Gaskiya ina gaya maku, sun samu ladansu.
Derfor, når du giver Almisse, må du ikke lade blæse i Basun foran dig, som Hyklerne gøre i Synagogerne og på Gaderne, for at de kunne blive ærede af Menneskene; sandelig, siger jeg eder, de have allerede fået deres Løn.
3 Amma in za ku yi sadaka, kada hannunku na hagu ya san abin da hannunku na dama yake yi,
Men når du giver Almisse, da lad din venstre Hånd ikke vide, hvad din højre gør,
4 domin sadakarku ta zama a asirce. Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.
for at din Almisse kan være i Løndom, og din Fader, som ser i Løndom, skal betale dig.
5 Sa'adda za ku yi addu'a kuma, kada ku zama kamar munafukai, domin sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'unsu da kuma a gefen tituna, domin mutane su gansu. Gaskiya ina gaya maku, sun sami ladarsu kenan.
Og når I bede, skulle I ikke være som Hyklerne; thi de stå gerne i Synagogerne og på Gadehjørnerne og bede, for at de kunne vise sig for Menneskene; sandelig, siger jeg eder, de have allerede fået deres Løn.
6 Amma ku, idan za ku yi addu'a, sai ku shiga cikin daki. Ku rufe kofa, ku yi addu'a ga Ubanku wanda yake a asirce, Ubanku kuwa da ke ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.
Men du, når du beder, da gå ind i dit Kammer, og luk din Dør, og bed til din Fader, som er i Løndom, og din Fader, som ser i Løndom, skal betale dig.
7 Idan za ku yi addu'a, kada ku yi ta maimaici marar anfani, kamar yadda al'ummai suke yi, domin a tunanin su za a saurare su saboda yawan maganganunsu.
Men når I bede, må I ikke bruge overflødige Ord som Hedningerne; thi de mene, at de skulle blive bønhørte for deres mange Ord.
8 Domin haka, kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatar ku tun kafin ku roke shi.
Ligner derfor ikke dem; thi eders Fader ved, hvad I trænge til, førend I bede ham,
9 Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka: 'Ubanmu da ke sama, bari a tsarkake sunanka.
Derfor skulle I bede således: Vor Fader, du, som er i Himlene! Helliget vorde dit Navn;
10 Bari mulkinka shi zo. Bari nufinka ya yiwu a duniya kamar yadda ake yi a sama.
komme dit Rige; ske din Villie, som i Himmelen således også på Jorden;
11 Ka ba mu yau abincinmu na kullum.
giv os i dag vort daglige Brød:
12 Ka gafarta mana basussukanmu, kamar yadda mu ma muke gafarta ma wadanda muke bi bashi.
og forlad os vor Skyld, som også vi forlade vore Skyldnere;
13 Kuma kada ka kawo mu cikin jaraba, amma ka kubutar da mu daga Mugun.' [Gama mulki da iko da daukaka naka ne har abada. Amin]
og led os ikke i Fristelse; men fri os fra det onde; (thi dit er Riget og Magten og Æren i Evighed! Amen.)
14 Domin in kun yafe wa mutane laifuffukansu, Ubanku na Sama shima zai yafe maku.
Thi forlade I Menneskene deres Overtrædelser, vil eders himmelske Fader også forlade eder;
15 In kuwa ba ku yafe wa mutane laifuffukansu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku laifuffukanku ba.”
men forlade I ikke Menneskene deres Overtrædelser, vil eders Fader ikke heller forlade eders Overtrædelser.
16 Haka kuma, in za ku yi azumi, kada ku zama da fuska kamar masu makoki yadda munafukai ke yi, domin sukan yankwane fuskokinsu, domin su bayyana ga mutane kamar suna azumi. Gaskiya, ina gaya maku, sun sami ladansu ke nan.
Og når I faste, da ser ikke bedrøvede ud som Hyklerne; thi de gøre deres Ansigter ukendelige, for at de kunne vise sig for Menneskene som fastende; sandelig, siger jeg eder, de have allerede fået deres Løn.
17 Amma in kuna azumi, ku shafa mai a ka, ku kuma wanke fuska,
Men du, når du faster, da salv dit Hoved, og to dit Ansigt,
18 don kada mutane su gane kuna azumi, sai dai Ubanku da yake a asirce. Kuma Ubanku da ke ganin abinda ke a asirce, zai saka maku.”
for at du ikke skal vise dig for Menneskene som fastende, men for din Fader, som er i Løndom; og din Fader, som ser i Løndom, skal betale dig.
19 “Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa ke batawa, inda barayi kuma ke fasawa su yi sata.
Samler eder ikke Skatte på Jorden, hvor Møl og Rust fortære, og hvor Tyve bryde ind og stjæle;
20 Maimakon haka, ku tara wa kanku dukiya a sama, inda babu asu da tsatsa da za su bata, inda kuma ba barayi da za su fasa su yi sata.
men samler eder Skatte i Himmelen, hvor hverken Møl eller Rust fortære, og hvor Tyve ikke bryde ind og stjæle.
21 Domin inda dukiyar ka take, a nan zuciyar ka ma take.
Thi hvor din Skat er, der vil også dit Hjerte være.
22 Ido shi ne fitilar jiki. Saboda haka, idan idonka na da kyau, dukan jiki na cike da haske.
Øjet er Legemets Lys; derfor, dersom dit Øje er sundt, bliver hele dit Legeme lyst;
23 Amma in idonka na da lahani, dukan jiki na cike da duhu. Saboda haka, in hasken da yake cikinka duhu ne, ina misalin yawan duhun!
men dersom dit Øje er dårligt, bliver hele dit Legeme mørkt. Dersom nu det Lys, der er i dig, er Mørke, hvor stort bliver da ikke Mørket!
24 Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya, ko kuma ya amince wa dayan ya raina dayan. Ba dama ku bauta wa Allah da kuma dukiya.
Ingen kan tjene to Herrer; thi han må enten hade den ene og elske den anden eller holde sig til den ene og ringeagte den anden. I kunne ikke tjene Gud og Mammon.
25 Saboda haka ina gaya maku, kada ku damu a kan rayuwarku, game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha- ko kuwa jikinku, abin da za ku yi tufafi da shi. Ashe rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
Derfor siger jeg eder: Bekymrer eder ikke for eders Liv, hvad I skulle spise, eller hvad I skulle drikke; ikke heller for eders Legeme, hvad I skulle iføre eder. Er ikke Livet mere end Maden, og Legemet mere end Klæderne?
26 Ku dubi tsuntsayen da ke sararin sama. Ai, ba su shuka, balle girbi, ba su kuma tarawa a cikin rumbuna, amma Ubanku na Sama na ciyar da su. Ashe, ba ku fi su martaba ba?
Ser på Himmelens Fugle; de så ikke og høste ikke og sanke ikke i Lader, og eders himmelske Fader føder dem; ere I ikke meget mere værd end de?
27 Kuma wanene a cikinku, don damuwarsa, zai iya kara ko taki ga tsawon rayuwarsa?
Og hvem af eder kan ved at bekymre sig lægge een Alen til sin Vækst?
28 To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi furannin jeji, yadda suke girma. Ba su aiki, kuma ba su sakar kaya.
Og hvorfor bekymre I eder for Klæder? Betragter Lillierne på Marken, hvorledes de vokse; de arbejde ikke og spinde ikke;
29 Duk da haka ina gaya maku, ko Sulaimanu ma, cikin dukan daukakar sa bai yi ado kamar daya daga cikin wadannan ba.
men jeg siger eder, at end ikke Salomon i al sin Herlighed var klædt som en af dem.
30 Idan Allah yayi wa ciyawar jeji ado, wadda yau tana wanzuwa, gobe kuwa a jefa ta cikin murhu, ina misalin adon da za ya yi maku, ya ku masu karancin bangaskiya?
Klæder da Gud således det Græs på Marken, som står i dag og i Morgen kastes i Ovnen, skulde han da ikke meget mere klæde eder, I lidettroende?
31 Don haka kada ku damu, kuna cewa, 'Me za mu ci? ko, Me za mu sha?' ko kuwa, 'Wadanne tufafi za mu sa?'
Derfor må I ikke bekymre eder og sige: Hvad skulle vi spise? eller: Hvad skulle vi drikke? eller: Hvormed skulle vi klæde os?
32 Ai, al'ummai ma suna neman dukan irin wadannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
- efter alt dette søge jo Hedningerne -. Thi eders himmelske Fader ved, at I have alle disse Ting nødig.
33 Amma ku nemi mulkinsa da farko da adalcinsa, kuma dukan wadannan abubuwa za a baku.
Men søger først Guds Rige og hans Retfærdighed, så skulle alle disse Ting gives eder i Tilgift.
34 “Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe za ta damu da kanta. Kowace rana ta na cike da wahalarta”.
Bekymrer eder derfor ikke for den Dag i Morgen; thi den Dag i Morgen skal bekymre sig for sig selv. Hver Dag har nok i sin Plage.