< Mattiyu 5 >
1 Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa.
Seeing the multitude of people, Jesus went up the Hill. There He seated Himself, and when His disciples came to Him,
2 Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa,
He proceeded to teach them, and said:
3 “Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne.
"Blessed are the poor in spirit, for to them belongs the Kingdom of the Heavens.
4 Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.
"Blessed are the mourners, for they shall be comforted.
5 Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya.
"Blessed are the meek, for they as heirs shall obtain possession of the earth.
6 Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su.
"Blessed are those who hunger and thirst for righteousness, for they shall be completely satisfied.
7 Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai.
"Blessed are the compassionate, for they shall receive compassion.
8 Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.
"Blessed are the pure in heart, for they shall see God.
9 Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah.
"Blessed are the peacemakers, for it is they who will be recognized as sons of God.
10 Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.
"Blessed are those who have borne persecution in the cause of Righteousness, for to them belongs the Kingdom of the Heavens.
11 Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni.
"Blessed are you when they have insulted and persecuted you, and have said every cruel thing about you falsely for my sake.
12 Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.
Be joyful and triumphant, because your reward is great in the Heavens; for so were the Prophets before you persecuted.
13 Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane.
"You are the salt of the earth; but if salt has become tasteless, in what way can it regain its saltness? It is no longer good for anything but to be thrown away and trodden on by the passers by.
14 Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.
You are the light of the world; a town cannot be hid if built on a hill-top.
15 Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan.
Nor is a lamp lighted to be put under a bushel, but on the lampstand; and then it gives light to all in the house.
16 Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.
Just so let your light shine before all men, in order that they may see your holy lives and may give glory to your Father who is in Heaven.
17 Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su.
"Do not for a moment suppose that I have come to abrogate the Law or the Prophets: I have not come to abrogate them but to give them their completion.
18 Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.
Solemnly I tell you that until Heaven and earth pass away, not one iota or smallest detail will pass away from the Law until all has taken place.
19 Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama.
Whoever therefore breaks one of these least commandments and teaches others to break them, will be called the least in the Kingdom of the Heavens; but whoever practises them and teaches them, he will be acknowledged as great in the Kingdom of the Heavens.
20 Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.
For I assure you that unless your righteousness greatly surpasses that of the Scribes and the Pharisees, you will certainly not find entrance into the Kingdom of the Heavens.
21 Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.'
"You have heard that it was said to the ancients, 'Thou shalt not commit murder', and whoever commits murder will be answerable to the magistrate.
22 Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama. (Geenna )
But I say to you that every one who becomes angry with his brother shall be answerable to the magistrate; that whoever says to his brother 'Raca,' shall be answerable to the Sanhedrin; and that whoever says, 'You fool!' shall be liable to the Gehenna of Fire. (Geenna )
23 Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai,
If therefore when you are offering your gift upon the altar, you remember that your brother has a grievance against you,
24 ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.
leave your gift there before the altar, and go and make friends with your brother first, and then return and proceed to offer your gift.
25 Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku.
Come to terms without delay with your opponent while you are yet with him on the way to the court; for fear he should obtain judgement from the magistrate against you, and the magistrate should give you in custody to the officer and you be thrown into prison.
26 Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.
I solemnly tell you that you will certainly not be released till you have paid the very last farthing.
27 Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'.
"You have heard that it was said, 'Thou shalt not commit adultery.'
28 Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.
But I tell you that whoever looks at a woman and cherishes lustful thoughts has already in his heart become guilty with regard to her.
29 Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. (Geenna )
If therefore your eye, even the right eye, is a snare to you, tear it out and away with it; it is better for you that one member should be destroyed rather than that your whole body should be thrown into Gehenna. (Geenna )
30 Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama. (Geenna )
And if your right hand is a snare to you, cut it off and away with it; it is better for you that one member should be destroyed rather than that your whole body should go into Gehenna. (Geenna )
31 An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.'
"It was also said, 'If any man puts away his wife, let him give her a written notice of divorce.'
32 Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.
But I tell you that every man who puts away his wife except on the ground of unfaithfulness causes her to commit adultery, and whoever marries her when so divorced commits adultery.
33 Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.'
"Again, you have heard that it was said to the ancients, 'Thou shalt not swear falsely, but shalt perform thy vows to the Lord.'
34 Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne;
But I tell you not to swear at all; neither by Heaven, for it is God's throne;
35 ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.
nor by the earth, for it is the footstool under His feet; nor by Jerusalem, for it is the City of the Great King.
36 Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba.
And do not swear by your head, for you cannot make one hair white or black.
37 Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.
But let your language be, 'Yes, yes,' or 'No, no.' Anything in excess of this comes from the Evil one.
38 Kun dai ji an ce, “Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.'
"You have heard that it was said, 'Eye for eye, tooth for tooth.'
39 Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.
But I tell you not to resist a wicked man, but if any one strikes you on the right cheek, turn the other to him as well.
40 Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma.
If any one wishes to go to law with you and to deprive you of your under garment, let him take your outer one also.
41 Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu.
And whoever shall compel you to convey his goods one mile, go with him two.
42 Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.
To him who asks, give: from him who would borrow, turn not away.
43 Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.'
"You have heard that it was said, 'Thou shalt love thy neighbour and hate thine enemy.'
44 Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku,
But I command you all, love your enemies, and pray for your persecutors;
45 domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.
that so you may become true sons of your Father in Heaven; for He causes His sun to rise on the wicked as well as the good, and sends rain upon those who do right and those who do wrong.
46 Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba?
For if you love only those who love you, what reward have you earned? Do not even the tax-gatherers do that?
47 Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba?
And if you salute only your near relatives, what praise is due to you? Do not even the Gentiles do the same?
48 Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.
You however are to be complete in goodness, as your Heavenly Father is complete.