< Mattiyu 5 >
1 Da Yesu ya ga taron jama'ar, sai ya hau saman dutse. Sa'adda ya zauna, almajiransa suka zo wurinsa.
And seeing great masses of people he went up into the mountain; and when he was seated his disciples came to him.
2 Ya bude bakinsa kuma ya koyar da su, yana cewa,
And with these words he gave them teaching, saying,
3 “Albarka ta tabbata ga masu talauci a ruhu, domin mulkin sama nasu ne.
Happy are the poor in spirit: for the kingdom of heaven is theirs.
4 Albarka ta tabbata ga masu makoki, domin za a ta'azantar da su.
Happy are those who are sad: for they will be comforted.
5 Albarka ta tabbata ga masu tawali'u, domin za su gaji duniya.
Happy are the gentle: for the earth will be their heritage.
6 Albarka ta tabbata ga masu yunwa da kishin adalci, domin za a kosar da su.
Happy are those whose heart's desire is for righteousness: for they will have their desire.
7 Albarka ta tabbata ga masu jinkai, domin za su samu jinkai.
Happy are those who have mercy: for they will be given mercy.
8 Albarka ta tabbata ga masu tsabtar zuciya, domin za su ga Allah.
Happy are the clean in heart: for they will see God.
9 Albarka ta tabbata ga masu kawo salama, domin za a ce da su 'ya'yan Allah.
Happy are the peacemakers: for they will be named sons of God.
10 Albarka ta tabbata ga wadanda ake tsananta masu saboda adalci, domin mulkin sama nasu ne.
Happy are those who are attacked on account of righteousness: for the kingdom of heaven will be theirs.
11 Masu albarka ne ku sa'adda mutane suka zage ku, suka kuma tsananta maku, ko kuwa suka zarge ku da dukan miyagun abubuwa iri iri na karya, saboda ni.
Happy are you when men give you a bad name, and are cruel to you, and say all evil things against you falsely, because of me.
12 Ku yi murna da matukar farin ciki, domin sakamakonku mai yawan gaske ne a sama. Ta haka ne mutane suka tsananta wa annabawa da suka yi rayuwa kafin ku.
Be glad and full of joy; for great is your reward in heaven: for so were the prophets attacked who were before you.
13 Ku ne gishirin duniya, amma idan gishiri ya sane yaya za a mai da dandanonsa? Ba zai kara anfani ga komai ba, sai ko a zubar da shi, a tattake a karkashin kafafun mutane.
You are the salt of the earth; but if its taste goes from the salt, how will you make it salt again? it is then good for nothing but to be put out and crushed under foot by men.
14 Ku ne hasken duniya, birnin da ke kan tudu ba shi boyuwa.
You are the light of the world. A town put on a hill may be seen by all.
15 Mutane ba za su kunna fitila su sa ta karkashin kwando ba, sai ko a dora ta a mazaunin ta, domin ta ba da haske ga kowa da ke gidan.
And a burning light is not put under a vessel, but on its table; so that its rays may be shining on all who are in the house.
16 Bari hasken ku ya haskaka gaban mutane yadda za su ga kyawawan ayyukanku su kuma yabi Ubanku da ke cikin sama.
Even so let your light be shining before men, so that they may see your good works and give glory to your Father in heaven.
17 Kada ku yi tsammanin na zo ne domin in rushe shari'a ko annabawa. Ban zo domin in rushe su ba, amma domin in cika su.
Let there be no thought that I have come to put an end to the law or the prophets. I have not come for destruction, but to make complete.
18 Domin gaskiya ina gaya maku, har sama da kasa su shude, amma digo ko wasali daya ba za ya shude ba a cikin shari'ar, sai an cika dukan al'amura.
Truly I say to you, Till heaven and earth come to an end, not the smallest letter or part of a letter will in any way be taken from the law, till all things are done.
19 Saboda haka duk wanda ya karya mafi kankanta daga cikin dokokin nan ko kuwa ya koya wa wasu su yi haka, za a kira shi mafi kankanta a cikin mulkin sama. Amma dukan wanda ya kiyaye su ko kuwa ya koyar da su, za a kira shi mafi girma a cikin mulkin sama.
Whoever then goes against the smallest of these laws, teaching men to do the same, will be named least in the kingdom of heaven; but he who keeps the laws, teaching others to keep them, will be named great in the kingdom of heaven.
20 Gama ina gaya maku cewa idan adalcin ku bai zarce adalcin marubuta da Farisawa ba, babu yadda za ku shiga mulkin sama.
For I say to you, If your righteousness is not greater than the righteousness of the scribes and Pharisees, you will never go into the kingdom of heaven.
21 Kun ji dai an ce wa mutanen da, 'Kada ka yi kisan kai,' kuma 'Duk wanda ya yi kisan kai yana cikin hatsarin hukunci.'
You have knowledge that it was said in old times, You may not put to death; and, Whoever puts to death will be in danger of being judged:
22 Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da dan'uwansa, yana cikin hatsarin hukunci. Kuma duk wanda ya ce da dan'uwansa, 'Kai mutumin banza!' yana cikin hatsarin tsayawa gaban majalisa, kowa kuma ya ce da dan'uwan sa 'Kai wawa!' yana cikin hatsarin shiga wutar jahannama. (Geenna )
But I say to you that everyone who is angry with his brother will be in danger of being judged; and he who says to his brother, Raca, will be in danger from the Sanhedrin; and whoever says, You foolish one, will be in danger of the hell of fire. (Geenna )
23 Saboda haka idan za ka yi baiko a bagadi sai ka tuna cewa dan'uwanka yana da damuwa da kai,
If then you are making an offering at the altar and there it comes to your mind that your brother has something against you,
24 ka bar baikon ka a gaban bagadin, ka yi tafiyarka. Da farko dai, ka sasanta da dan'uwanka kafin ka zo ka mika baikon.
While your offering is still before the altar, first go and make peace with your brother, then come and make your offering.
25 Ka yi sulhu da mai karar ka tun kana hanyar zuwa gaban shari'a, domin kada mai karar ka ya mika ka ga alkali, alkali kuwa ya mika ka ga dogarai, za a kuwa jefa ka a kurkuku.
Come to an agreement quickly with him who has a cause against you at law, while you are with him on the way, for fear that he may give you up to the judge and the judge may give you to the police and you may be put into prison.
26 Gaskiya ina gaya maka, ba za ka taba fita daga can ba sai ko ka biya dukan kudin da ya ke binka.
Truly I say to you, You will not come out from there till you have made payment of the very last farthing.
27 Kun dai ji an ce, 'Kada ka yi zina'.
You have knowledge that it was said, You may not have connection with another man's wife:
28 Amma ina gaya maku, duk wanda ya dubi mace, da muguwar sha'awa, ya riga ya yi zina da ita a zuciyarsa.
But I say to you that everyone whose eyes are turned on a woman with desire has had connection with her in his heart.
29 Idan idonka na dama zai sa ka tuntube, kwakule shi ka jefar daga gareka. Don gara daya daga cikin gabobinka ya halaka, da a jefa dukan jikin ka a jahannama. (Geenna )
And if your right eye is a cause of trouble to you, take it out and put it away from you; because it is better to undergo the loss of one part, than for all your body to go into hell. (Geenna )
30 Ko kuwa idan hannunka na dama zai sa ka tuntube, ka yanke shi ka jefar daga gare ka. Domin gara daya daga cikin gabobin ka ya halaka, da a jefa dukan jikinka a jahannama. (Geenna )
And if your right hand is a cause of trouble to you, let it be cut off and put it away from you; because it is better to undergo the loss of one part, than for all your body to go into hell. (Geenna )
31 An sake fada, 'Duk wanda ya kori matarsa, sai ya ba ta takaddar saki.'
Again, it was said, Whoever puts away his wife has to give her a statement in writing for this purpose:
32 Amma ina gaya maku ko wa ya saki matarsa, idan ba a kan laifin lalata ba, ya mai da ita mazinaciya kenan. Kuma duk wanda ya aure ta bayan sakin, ya yi zina kenan.
But I say to you that everyone who puts away his wife for any other cause but the loss of her virtue, makes her false to her husband; and whoever takes her as his wife after she is put away, is no true husband to her.
33 Kun sake ji an ce wa wadan da suke a zamanin da, 'Kada ku yi rantsuwar karya, amma ku yi rantsuwar ku ga Ubangiji.'
Again, you have knowledge that it was said in old times, Do not take false oaths, but give effect to your oaths to the Lord:
34 Amma ina gaya maku, kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama domin kursuyin Allah ne;
But I say to you, Take no oaths at all: not by the heaven, because it is the seat of God;
35 ko kuwa da duniya, domin mazaunin kafafunsa ne, ko da Urushalima, domin birnin babban sarki ne.
Or by the earth, because it is the resting-place for his foot; or by Jerusalem, because it is the town of the great King.
36 Ko ma ace ku yi rantsuwa da kanku, domin ba za ku iya mai da gashin kanku baki ko fari ba.
You may not take an oath by your head, because you are not able to make one hair white or black.
37 Amma bari maganarku ta zama 'I, I', ko kuwa 'A'a, a'a.' Duk abin da ya wuce wannan, daga mugun yake.
But let your words be simply, Yes or No: and whatever is more than these is of the Evil One.
38 Kun dai ji an ce, “Ido a maimakon ido, hakori kuma a maimakon hakori.'
You have knowledge that it was said, An eye for an eye, and a tooth for a tooth:
39 Amma ina gaya maku, kada ku yi jayayya da wanda ke mugu, a maimakon haka, ko wa ya mare ku a kuncin dama, ku juya masa dayan ma.
But I say to you, Do not make use of force against an evil man; but to him who gives you a blow on the right side of your face let the left be turned.
40 Idan wani yana da niyyar kai kararku gaban shari'a saboda ya karbi rigarku, ku ba wannan mutumin mayafinku ma.
And if any man goes to law with you and takes away your coat, do not keep back your robe from him.
41 Duk wanda ya tilasta ku ga tafiyar mil daya, ku je da shi biyu.
And whoever makes you go one mile, go with him two.
42 Ku ba kowa da ya tambaye ku, kuma kada ku hana kowa da ke neman rance a wurinku.
Give to him who comes with a request, and keep not your property from him who would for a time make use of it.
43 Kun ji abin da aka fada, 'Za ka kaunaci makwabcin ka ka ki magabcin ka.'
You have knowledge that it was said, Have love for your neighbour, and hate for him who is against you:
44 Amma ina gaya maku, ku kaunaci magabtan ku, ku yi addu'a domin masu tsananta maku, ku albarkaci wadanda suka la'ance ku, ku yi alheri ga wadanda suke kin ku,
But I say to you, Have love for those who are against you, and make prayer for those who are cruel to you;
45 domin ku zama 'ya'yan Ubanku da ke cikin sama. Domin yakan sa rana ta haskaka wa mugu da mutumin kirki, kuma yakan aiko da ruwan sama ga adali da azzalumi.
So that you may be the sons of your Father in heaven; for his sun gives light to the evil and to the good, and he sends rain on the upright man and on the sinner.
46 Domin idan kuna kaunar wadanda suke kaunarku, wanne lada kuka samu? Ba haka masu karban haraji ma suke yi ba?
For if you have love for those who have love for you, what credit is it to you? do not the tax-farmers the same?
47 Kuma in kun gaida 'yan'uwanku kadai, me kuke yi fiye da sauran? Ba hakanan al'ummai ma suke yi ba?
And if you say, Good day, to your brothers only, what do you do more than others? do not even the Gentiles the same?
48 Saboda haka, lalle ne ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na sama yake cikakke.
Be then complete in righteousness, even as your Father in heaven is complete.