< Mattiyu 4 >

1 Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
Etu pichete Jisu ke Atma pora ekta sunsan jagate loi jaise juntu jagate saitan pora taike porikha koribo.
2 Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
Aru chalis din aru chalis rati Jisu upwas korise, etu karone Tai bhuk lagi jaise.
3 Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
Titia porikha kora jon ahikena Taike eneka koise, “Apuni Isor laga Putro ase koile, etu pathor khan ke roti hobole kobi.”
4 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
Kintu Jisu taike jowab dikena koise, “Isor kotha te eneka likhi kene ase, ‘Manu to khali bhaat khaikena jinda nathake, kintu Isor laga mukh pora ula kotha te he jinda thakibo.’”
5 Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
Etu pichete saitan pora Jisu ke pobitro sheher te loi jaise aru mondoli laga sob pora uporte khara koribo dise,
6 ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
aru Taike koise, “Apuni Isor laga Putro ase koile, yate pora nijorke nichete phelai dibi, kele koile Isor laga kotha te eneka likha ase, ‘Tai pora Tai laga duth khan ke hukum dikene Apuni ke bachai lobo,’ Aru, ‘Taikhan laga hath pora Apuni ke dhuri lobo, Aru Apuni laga theng ke pathor pora bhi jokhom nahobo.’”
7 Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
Jisu taike eneka koise, “Aru Isor kotha te etu bhi likhi kene ase, ‘Apuni laga Probhu Isor ke porikha na koribi.’”
8 Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
Aru, saitan pora Jisu ke untcha pahar te loi jaise aru Taike prithibi laga rajyokhan laga dangor mohima thaka dikhai dise.
9 Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
Saitan pora Taike koise, “Apuni moike athukari kene aradhana korile, eitu khan sob ami Apnike di dibo.”
10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
Titia Jisu pora taike koise, “Yate pora jai jabi, Saitan! Kilekoile Shastro te eneka likhi kene ase, ‘Tumikhan khali Probhu, tumi laga Isor ke he aradhana koribi, aru khali Taike he sewa koribi.’”
11 Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
Titia saitan Taike chari kene jai jaise, aru sabi, sorgodoth khan ahi kene Taike modot korise.
12 To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
Jitia John ke dhurise koi kene Jisu khobor paise, Tai Galilee jagate wapas jai jaise.
13 Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
Tai Nazareth sheher chari kene Galilee Samundar laga usorte thaka, Capernaum town te jaise, etu jaga to Zebulun aru Naphtali laga majot te ase.
14 Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
Isaiah bhabobadi dwara Isor kotha pora kowa pura hobole karone eitu khan sob eneka hoise,
15 “Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
“Zebulun laga mati aru Naphtali laga mati, Sagar phale, Jordan paar kori kene, Porjati khan laga Galilee!
16 Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
Utu manu khan jun andhera te bohi thake taikhan dangor ekta ujala dikhise, Aru jun khan mora laga chaya aru jagate bohi thake, Taikhan uporte ekta pohor dikhai dise.”
17 Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
Utu somoi pora he Jisu prochar kori bole shuru hoise aru koise, “Mon ghura bhi, kele koile sorgo laga rajyo to usor hoise.”
18 Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
Jitia Tai Galilee Nodi phale berai thakisele, Tai Simon junke Peter koi, aru tai laga bhai Andrew khan ke maas dhora jaal loi kene samundar te phelai thaka dikhise, kele koile taikhan maas dhora manu thakise.
19 Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
Jisu taikhan ke koise, “Ahibi, Ami laga piche koribi, aru Moi tumikhan ke manu dhori bole bonai dibo.”
20 Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
Loge-loge taikhan laga maas dhura jaal khan phelai dise aru Jisu laga piche kori bole shuru hoise.
21 Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
Jitia Jisu ta te pora jai thakise, tai duijon bhai ke dikhise, James, Zebedee laga chokra, aru tai laga bhai John Tai ekta naw te taikhan laga baba Zebedee logote maas dhura jaal khan milai thakise. Jisu taikhan ke matise,
22 Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
Aru etu loge-loge taikhan laga naw aru baba ke chari kene Jisu laga piche korise.
23 Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
Titia Jisu Galilee laga sob jagate berai jaise, synagogue khan te sikhaise, aru rajyo laga susamachar prochar korise, aru sob kisim laga ghao bemar aru bemar manu khan ke changai korise.
24 Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
Tai laga khobor sob Syria jagate punchi jaise, aru manu khan Jisu usorte kisim-kisim bemar pora dukh pai thaka khan, gaw bhitor te bhoot huma khan, murgi-bemar thaka khan, aru jothor bemar thaka khan sobke loi kene anise. Aru taikhan ke Jisu pora changai kori dise.
25 Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
Aru Galilee, Decapolis, Jerusalem, Judea, aru Jordan pora bhi dur thaka sob jaga pora manu khan Jisu logot ahise.

< Mattiyu 4 >