< Mattiyu 4 >

1 Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
Alors Jésus fut emmené par l'Esprit au désert, pour être tenté par le diable.
2 Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
Il jeûna quarante jours et quarante nuits, après quoi il eut faim.
3 Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
Et le tentateur l'ayant abordé, lui dit: «Si tu es Fils de Dieu, ordonne que ces pierres se changent en pains.»
4 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
Mais Jésus répondit: Il est écrit: «l’homme ne vivra pas de pain seulement, mais de toute parole qui sort de la bouche de Dieu.»
5 Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
Alors le diable le transporta dans la ville sainte, le posa à l'extrémité de l'aile du temple,
6 ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
et lui dit: «Si tu es Fils de Dieu, jette-toi en bas; car il est écrit: «Il donnera des «ordres à ses anges, à ton sujet; et ils te porteront sur leurs bras, de peur que ton pied ne heurte contre une pierre.»
7 Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
Jésus lui dit: Il est écrit aussi: «Tu ne tenteras point le Seigneur ton Dieu.»
8 Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
Le diable le transporta encore sur une montagne très-haute, lui montra tous les royaumes du monde et leur gloire,
9 Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
et lui dit: «Je te donnerai tout cela, si, te jetant à mes pieds, tu m'adores.»
10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
Jésus lui dit: Retire-toi, Satan; car il est écrit: «Tu adoreras le Seigneur ton Dieu, et tu le serviras lui seul.»
11 Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
Alors le diable le quitta; et des anges s'approchèrent, et ils le servirent.
12 To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
Jésus ayant appris que Jean avait été mis en prison, se retira en Galilée.
13 Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
Il quitta Nazareth et alla s'établir à Capernaoum, ville située au bord de la mer, dans le territoire de Zabulon et de Nephthali,
14 Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
afin que s'accomplît ce qui a été dit par Esaïe, le prophète:
15 “Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
«La terre de Zabulon et la terre de Nephthali, ce pays qui s’étend vers la mer jusqu'au delà du Jourdain, la Galilée des Gentils,
16 Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
ce pays, qui était plongé dans les ténèbres, a vu une grande lumière, et la lumière s'est levée sur ceux qui étaient dans la région et dans l’ombre de la mort.»
17 Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
Dès lors Jésus se mit à prêcher, disant: «Repentez-vous, car le royaume des cieux est proche.»
18 Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
Comme il cheminait le long de la mer de Galilée, il vit deux frères, Simon, appelé Pierre, et André, son frère, qui jetaient leurs filets dans la mer, car ils étaient pêcheurs.
19 Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
Et il leur dit: «Venez, suivez-moi, et je vous ferai pêcheurs d'hommes.»
20 Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
Aussitôt ils quittèrent leurs filets, et le suivirent.
21 Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
Puis, un peu plus loin, il vit deux autres frères, Jacques, fils de Zébédée, et Jean, son frère, qui raccommodaient leurs filets dans leur barque avec Zébédée leur père, et il les appela.
22 Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
Aussitôt ils quittèrent leur barque et leur père, et le suivirent.
23 Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
Jésus allait par toute la Galilée, enseignant dans les synagogues, prêchant la bonne nouvelle du royaume et guérissant
24 Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
toute maladie et toute infirmité parmi le peuple. Sa renommée se répandit dans toute la Syrie, et on lui amena tous ceux qui se portaient mal, qui étaient affligés de maladies et de douleurs diverses, des démoniaques, des lunatiques, des paralytiques, et il les guérit.
25 Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
Une grande foule le suivit de la Galilée, de la Décapole, de Jérusalem, de la Judée et d'au delà du Jourdain.

< Mattiyu 4 >