< Mattiyu 4 >
1 Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
Siis juhtis Vaim Jeesuse kõrbe kuradi kiusata.
2 Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
Kui ta oli nelikümmend päeva ja nelikümmend ööd paastunud, tuli talle nälg.
3 Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
Talle lähenes kiusaja ning ütles: „Kui sa oled Jumala Poeg, siis käsi sellel kivil siin muutuda leivaks!“
4 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
Jeesus vastas: „Kirjutatud on: „Inimene ei ela üksnes leivast, vaid igast sõnast, mis lähtub Jumala suust.““
5 Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
Siis viis kurat ta pühasse linna, pani seisma templi katusele
6 ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
ja ütles: „Kui sa oled Jumala Poeg, siis kukuta end siit alla! Sest kirjutatud on: „Sinu pärast annab ta oma inglitele käsu ja nemad kannavad sind kätel, et sa oma jalga vastu kivi ei lööks.““
7 Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
Jeesus vastas talle: „Samuti on kirjutatud: „Ära pane Issandat, oma Jumalat, proovile!““
8 Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
Veel võttis kurat ta kaasa väga kõrge mäe otsa ja näitas talle kõiki maailma kuningriike ja nende hiilgust.
9 Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
„Need kõik ma annan sulle, “ütles ta, „kui sa ainult maha langed ja mind ülistad.“
10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
Siis ütles Jeesus talle: „Hoia minust eemale, saatan! Kirjutatud on: „Kummarda Issandat, oma Jumalat, ja teeni ainult teda!““
11 Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
Siis jättis kurat ta rahule. Seejärel tulid tema juurde inglid ja teenisid teda.
12 To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
Kui Jeesus kuulis, et Johannes on kinni võetud, läks ta tagasi Galileasse.
13 Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
Ta lahkus Naatsaretist ja asus elama Kapernauma, mis on järve ääres Sebuloni ja Naftali aladel.
14 Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
Nõnda läks täide, mis oli öeldud prohvet Jesaja suu läbi:
15 “Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
„Sebulonimaa ja Naftalimaa, teel mere äärde, piki Jordanit, rahvaste Galilea,
16 Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
rahvas, kes elab pimeduses, on suurt valgust näinud; neile, kes on elanud surma varjus, on koitnud valgus.“
17 Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
Sellest ajast peale hakkas Jeesus kuulutama: „Parandage meelt, sest taevariik on lähedal!“
18 Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
Kõndides Galilea mere rannal, nägi Jeesus kaht venda, Siimonit, hüüdnimega Peetrus, ja tema venda Andreast võrku merre heitmas, sest nad olid kalurid.
19 Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
Jeesus ütles neile: „Järgnege mulle ja ma teen teist inimestepüüdjad!“
20 Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
Nad jätsid kohe oma võrgud ja järgnesid talle.
21 Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
Sealt edasi minnes nägi ta veel kaht venda, Sebedeuse poega Jaakobust ja tema venda Johannest koos isaga paadis võrke parandamas. Jeesus kutsus ka neid.
22 Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
Kohe jätsid nad paadi ja isa maha ning järgnesid talle.
23 Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
Ja Jeesus rändas ringi kogu Galileas, õpetas sünagoogides, kuulutas evangeeliumi Kuningriigist ning tervendas rahvast igasugustest haigustest ja hädadest.
24 Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
Kuuldus temast levis kogu Süürias ning tema juurde toodi kõik, kes kannatasid mitmesuguste haiguste ja valude käes, kurjadest vaimudest vaevatuid, langetõbiseid ja halvatuid – ning tema tegi nad terveks.
25 Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
Ja Jeesuse kannul käis suur rahvahulk Galileast, Dekapolisest, Jeruusalemmast, Juudamaalt ja Jordani tagant.