< Mattiyu 4 >

1 Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
Then was Iesus ledd awaye of ye spirite into wildernes to be tempted of ye devyll.
2 Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
And when he had fasted fourtye dayes and fourtye nightes he was afterward an hungred.
3 Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
Then came to hym the tempter and sayde: yf thou be the sonne of God commaunde that these stones be made breed.
4 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
He answered and sayde: yt is wrytten man shall not lyve by brede onlye but by every worde yt proceadeth out of the mouth of God.
5 Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
Then the devyll tooke hym vp into ye holy cite and set hym on a pynacle of the teple
6 ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
and sayd vnto hym: yf thou be the sonne of God cast thy sylfe doune. For it is wrytte he shall geve his angels charge over the and with their handes they shall holde yt vp that thou dashe not thy fote agaynst a stone.
7 Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
And Iesus sayde to hym it ys wrytten also: Thou shalt not tempte thy Lorde God.
8 Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
The devyll toke hym vp agayne and ledde hym in to an excedynge hye mountayne and shewed hym all the kyngdomes of ye worlde and all ye glorie of them
9 Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
and sayde to hym: all these will I geue ye if thou wilt faull doune and worship me.
10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
Then sayde Iesus vnto hym. Avoyd Satan. For it is writte thou shalt worshyp ye Lorde thy God and hym only shalt thou serve.
11 Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
Then the dyvell left hym and beholde the angels came and ministred vnto hym.
12 To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
When Iesus had hearde yt Ihon was taken he departed into Galile
13 Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
and left Nazareth and went and dwelte in Capernaum which is a cite apon the see in ye coostes of zabulon and Neptalim
14 Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
to fulfill that whiche was spoken by Esay the Prophet sayinge:
15 “Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
The londe of zabulon and Neptalim the waye of the see beyonde Iordan Galile of the Gentyls
16 Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
ye people which sat in darknes sawe greate lyght and to them which sate in the region and shadowe of deeth lyght is begone to shyne.
17 Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
From yt tyme Iesus begane to preache and to saye: repet for ye kigdome of heve is at hode.
18 Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
As Iesus walked by the see of Galile he sawe two brethren: Simon which was called Peter and Andrew his brother castynge a neet into the see for they were fisshers
19 Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
and he sayde vnto them folowe me and I will make you fisshers of men.
20 Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
And they strayght waye lefte their nettes and folowed hym.
21 Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
And he went forthe from thence and sawe other twoo brethren Iames the sonne of zebede and Ihon his brother in the shippe with zebede their father mendynge their nettes and called them.
22 Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
And they with out taryinge lefte the shyp and their father and folowed hym.
23 Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
And Iesus went aboute all Galile teachyng in their synagoges and preachynge ye gospell of the kyngdome and healed all maner of sicknes and all maner dyseases amoge ye people.
24 Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
And his fame spreed abroode through oute all Siria. And they brought vnto hym all sicke people that were taken with divers diseases and gripinges and them yt were possessed with devils and those which were lunatyke and those that had the palsie: and he healed the.
25 Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
And ther folowed hym a greate nombre of people from Galile and from the ten cyties and from Ierusalem and from Iury and from ye regions that lye beyonde Iordan.

< Mattiyu 4 >