< Mattiyu 4 >
1 Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
Then Jesus was led up into the desert by the Spirit, to be tempted by the devil.
2 Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
And after he had fasted forty days and forty nights, he became hungry,
3 Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
So the tempter came and said to him, "If you are the Son of God, bid these stones to become bread."
4 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
Jesus answered him, "It is written, Not by bread alone shall man live, but by every word that comes from the mouth of God."
5 Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
Then the devil took him up into the Holy City and stood him on the parapet of the temple,
6 ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
and said to him. "If you are the Son of God, throw yourself down; for it is written, "He will give his angels charge over thee; Upon their hands they will bear thee up, Lest thou dash thy foot against a stone."
7 Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
"It is written again," answered Jesus, "Thou shalt not tempt the Lord thy God."
8 Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
Then the devil took Jesus to a very high mountain, and showed all the kingdoms of the earth and the glory of them,
9 Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
and said to him, "All these will I give you, if you will fall down and worship me."
10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
"Begone, Satan!" answered Jesus, "for it is written, "Thou must worship the Lord thy God, and Him only must thou serve."
11 Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
Then the devil left him, and behold! angels came and began ministering to him.
12 To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
Now when Jesus heard that Johnhad been arrested, he withdrew into Galilee.
13 Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
He left Nazareth, and settled in Capernaum-by-the-Lake, near the borders of Zebulun and Naphtali,
14 Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
in order that these words spoken through Isaiah the prophet, might be fulfilled.
15 “Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
Land of Zebulun, land of Naphtali; The road by the Lake; the country beyond Jordan; Galilee of the Gentiles!
16 Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
The people who were dwelling in darkness Have seen a great light; And on those who were dwelling in the land of the shadows of death Light has dawned.
17 Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
From that time Jesus began to preach, saying, "Repent for the kingdom of heaven is near."
18 Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
And as he was walking by the see of Galilee, he saw two brothers- Simon who is called Peter, and Andrew, his brother-casting their net into the sea, for they were fishermen.
19 Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
"Come, follow me," said Jesus, "And I will make you fishers of men."
20 Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
And they dropped their nets at once, and followed him.
21 Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
As he went farther on he saw two other brothers, Jamesthe son of Zebedee, and Johnhis brother, in the boat with Zebedee their father, mending their nets, and he called them.
22 Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
They immediately left the boat and their father, and followed him.
23 Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
Then Jesus went about through Galilee, teaching in the synagogues, and preaching the gospel of the kingdom, and healing every kind of disease and infirmity among the people.
24 Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
And his fame spread throughout all Syria. They brought all the sick to him, those who were suffering from various diseases and troubles- demoniacs, epileptics, paralytics-and he healed them.
25 Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.
Great crowds followed him from Galilee, from the ten towns, from Jerusalem, and Judea, and from beyond Jordan.