< Mattiyu 27 >

1 Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
Very early the next morning all the chief priests and Jewish elders decided how [to arrange for the Romans] to execute Jesus.
2 Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
They tied his hands and took him to Pilate, the [Roman] governor.
3 Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
When Judas, the one who had (betrayed/enabled Jesus’ enemies to seize) him, realized that they had decided to have Jesus executed, he was very sorry [about what he had done]. He took the 30 coins back to the chief priests and elders.
4 yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
He said, “I have sinned. I have (betrayed/enabled you to seize) a man who (is innocent/has not done anything wrong).” They replied, “(That means nothing to us!/What does that mean to us?) [RHQ] That is your problem!”
5 Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
So Judas [took] the money [and] threw it inside the Temple. Then he went away and hanged himself.
6 Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
[Later] the high priests [found] the coins. They picked them up and said, “This is money that we paid [to have a man killed] [MTY], and our law does not allow [such money] to be put {us to put [such money]} into the [Temple treasury].”
7 Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
So they decided to use that money to buy the field where clay was dug for making pots {men dug ground for making pots}. [They made that field] a place where they buried strangers [who died in Jerusalem].
8 Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
That is why that place is still called {why they still call that place} ‘The field of blood’.
9 Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
[By buying that field], they fulfilled these words that the prophet Jeremiah wrote [long ago]: They took the 30 silver coins; That was what the leaders of Israel decided [that he was worth];
10 suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
and with that money they bought the field where clay was dug for potters. They did that as the Lord had commanded me.
11 Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
Jesus stood in front of [Pilate], the governor. The governor asked Jesus, “Do you [claim to be] the king of the Jews?” Jesus replied, “[It is] as you have [just] said.”
12 Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
When he was accused by the chief priests and elders {When the chief priests and elders accused him} about various things, he did not answer.
13 Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
So Pilate said to him, “You hear how many things they are saying to accuse you; [are you not going to reply]?”
14 Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
But [even though he was not guilty], Jesus did not say anything. He did not reply to any of the things about which they were accusing him. As a result, the governor was very surprised.
15 To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
It was the governor’s custom [each year] during the [Passover] celebration to release [one person who was in prison]. [He released] whichever prisoner the people wanted.
16 A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
At that time there was [in Jerusalem] a well-known prisoner whose name was Barabbas.
17 To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
So when the crowd gathered, Pilate asked them, “Which [prisoner] would you like me to release for you: Barabbas, or Jesus, whom [some of you] claim to be the Messiah?”
18 Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
[He asked that question] because he realized that the chief priests [wanted to have Jesus executed]. They had brought Jesus to him [only] because they were jealous of Jesus. [And Pilate thought that the crowd would prefer that he release Jesus].
19 Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
While Pilate was sitting on the platform [where he made] judicial [decisions], his wife sent him [this message]: “Early this morning I had a bad dream because of that man. So do not condemn that righteous man!”
20 A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
But the chief priests and elders persuaded the crowd to ask [Pilate to] release Barabbas, and to [order] that Jesus be executed {that [his soldiers] execute Jesus}.
21 Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
So when the governor asked them, “Which of the two men do you want me to release for you?” They replied, “Barabbas!”
22 Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
Pilate, [very astonished], asked, “So what shall I do with Jesus who [some of you] say is the Messiah?” They all answered, “[Command that] he be crucified! {[Command your soldiers] (to crucify him/to nail him to a cross)}!”
23 Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
Pilate replied, “Why? What crime has he committed?” But they shouted even louder, “[Have] him crucified {[Command that your soldiers] crucify him}!”
24 Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
Pilate realized that he was accomplishing nothing. He saw that instead, the people were starting to riot. So he took [a basin of] water and washed his hands as the crowd was watching. He said, “[By washing my hands I am showing you that] if this man dies [MTY], it is [your] fault, [not mine]!”
25 Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
And all the people answered, “The guilt for causing him to die [MTY] will be on us, and it will be on our children, too!”
26 Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
Then he [ordered the soldiers to] release Barabbas for them. But he [ordered that his soldiers] flog Jesus. And then he turned Jesus over to the soldiers for them (to nail Jesus to a cross/to crucify him).
27 Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
Then the governor’s soldiers took Jesus into the government headquarters. The whole (cohort/group of soldiers) gathered around him.
28 Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
They pulled off [his clothes], and [pretending he was a king, they] put a purple robe on him.
29 Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
They [took some branches with] thorns and wove them to make a crown and put it on his head. They put in his right hand a reed [like a staff that a king would hold]. Then they knelt in front of him and made fun of him, saying, “Hooray for the king of the Jews [IRO]!”
30 Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
They kept spitting on him. They took the staff and kept striking him on the head with it.
31 Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
When they had finished ridiculing him, they pulled off the robe and put his own clothes on him. Then they led him away to [the place where they] would nail him to a cross.
32 Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
[After Jesus carried his cross] a short distance, [the soldiers] saw a man named Simon, [who was] from Cyrene [city]. They forced him to carry the cross for Jesus.
33 Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
They came to a place called Golgotha. That name means ‘the place [like] a skull’.
34 Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
When [they got there], they mixed with wine something that tasted very bitter. They gave it to [Jesus] to drink [so that he would not feel so much pain when they nailed him on the cross]. But when he tasted it, he refused to drink it. [Some soldiers took his clothes].
35 Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
Then they nailed him to the cross. Afterwards, they divided his clothes among themselves by gambling with something like dice [to decide which piece of clothing each one would get].
36 Suka kuma zauna suna kallonsa.
Then the soldiers sat down there to guard him, [to prevent anyone from trying to rescue him].
37 A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
They fastened [to the cross] above Jesus’ head a [sign on which had been] {[they had]} written why [they] were nailing him to the cross. [But all] it said was, ‘This is Jesus, the King of the Jews’.
38 An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
Two bandits were also nailed {They also nailed two bandits} on crosses. One was nailed to a cross on the right side [of Jesus] and one to a cross on the left side.
39 Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
The people who were passing by insulted him by shaking their heads [as if he were an evil man].
40 suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
They said, “You [said you] would destroy the Temple, and then you would build it again within three days! [So if you could do that], you [should be able to] save yourself! If you are the man who is also God (OR, If you are the Son of God), come down from the cross!”
41 Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
Similarly, the chief priests, the men who taught the [Jewish] laws and the elders made fun of him. [Various ones of them] said things like,
42 “Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
“He [claims that he] saved others [IRO] [from their sicknesses], but he cannot help himself!” “He [says that he] is [IRO] the King of Israel. So he should come down from the cross. Then we would believe him!”
43 Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
“He [says that he] trusts in God, and that he is the man who is also God. So if God is pleased with him, God should rescue him now!”
44 Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
And the [two] bandits who had been crucified with him also insulted him, saying similar things.
45 To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
At noon it became dark over the whole land. [It stayed dark] until three o’clock [in the afternoon].
46 Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
At about three o’clock Jesus shouted loudly, “Eli, Eli, lama sabachthani?” That means, ‘My God, my God, why have you deserted me?’
47 Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
When some of the people standing there heard [the word ‘Eli’, misunderstanding it], they said, “He is calling for [the prophet] Elijah!”
48 Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
Immediately one of them ran and got a sponge. He filled it with sour wine. Then he put the sponge on [the tip of] a reed and [held it up in order that Jesus] could suck out [the wine that was in it].
49 Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
But the other [people there] said, “Wait! Let’s see if Elijah comes to save him!”
50 Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
Then after Jesus shouted out loudly again, he died, giving his spirit over [to God].
51 Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
At that moment the [heavy thick] curtain [that closed off the most holy place] in the Temple split into two pieces from top to bottom. [That signified that ordinary people could now go into the presence of God]. The earth shook, and [some large] rocks split open.
52 Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
[Some] tombs opened up, and the bodies of many godly people who had died became alive again.
53 Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
They came out of the tombs, and after Jesus became alive again, they went into Jerusalem and appeared to many people [there].
54 Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
The officer who supervised the soldiers [who nailed Jesus to the cross was standing nearby]. His soldiers who had been on guard [so that no one would rescue] Jesus [were also there]. When they [felt] the earthquake and saw all the [other] things that happened, they were terrified. They exclaimed, “Truly he was both man and God! (OR, a Son of God).”
55 Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
Many women were there, watching from a distance. They were women who had accompanied Jesus from Galilee [district] in order to provide the things he needed.
56 A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
Among these women were Mary from Magdala [town], [another] Mary who was the mother of James and Joseph, and the mother of James and John.
57 Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
When it was [almost] evening, a rich man named Joseph came [there]. He was from Arimathea [town]. He also was a disciple of Jesus.
58 Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
He then went to Pilate and asked Pilate to [allow him to take] the body of Jesus [and bury it]. Pilate ordered that [he] be allowed to {[his soldiers] let [Joseph]} take [the body].
59 Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
So Joseph [and others] took the body and wrapped it in a clean white cloth.
60 sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
Then they placed it in Joseph’s own new tomb that had been dug out of the rock [cliff]. They rolled a huge [circular flat] stone in front of the entrance to the tomb. Then they left.
61 Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
Mary from Magdala and the other Mary were sitting there opposite the tomb, [watching].
62 Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
The next day was Saturday, the Jewish day of rest. The chief priests and [some of] the Pharisees went to Pilate.
63 Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
They said, “Sir, we remember that while that deceiver was still alive, he said, ‘Three days after I [die I] will become alive again.’
64 Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
So we ask you to order that the tomb be guarded {that [soldiers] guard the tomb} for three days. If you do not do that, his disciples may come and steal the body. Then they will tell people that he has risen from the dead. If they deceive [people by saying that], it will be worse than the way he deceived people before [by saying that he was the Messiah].”
65 Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
Pilate replied, “You [can] take some soldiers. Go to the tomb and make it as secure as you know how.”
66 Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.
So they went and made the tomb secure by [fastening a cord from] the stone [that was in front of the entrance to the rock cliff on each side] and sealing it. They also [left some soldiers there to] guard [the tomb].

< Mattiyu 27 >