< Mattiyu 27 >
1 Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
Now when morning came, all the chief priests and the elders of the people took counsel against Jesus to put him to death.
2 Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
They bound him, led him away, and handed him over to Pontius Pilate, the governor.
3 Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
When Judas, who had betrayed him, saw that Jesus had been condemned, he regretted what he had done and returned the thirty pieces of silver to the chief priests and the elders,
4 yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
saying, “I have sinned by betraying innocent blood.” But they said, “What is that to us? See to it yoʋrself.”
5 Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
So he threw the pieces of silver into the temple and departed. Then he went away and hanged himself.
6 Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
The chief priests took the pieces of silver and said, “It is not lawful to put them into the temple treasury, since they are a price paid for blood.”
7 Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
So they took counsel and used the money to buy the potter's field as a burial place for foreigners.
8 Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
Therefore that field has been called the Field of Blood to this day.
9 Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
Then what was spoken by the prophet Jeremiah was fulfilled: “They took the thirty pieces of silver, the price of him on whom a price had been set, on whom some of the sons of Israel had set a price,
10 suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
and they gave them for the potter's field, as the Lord directed me.”
11 Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
Meanwhile, Jesus stood before the governor, and the governor asked him, “Are yoʋ the king of the Jews?” Jesus said to him, “Yoʋ have said it yoʋrself.”
12 Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
But when he was accused by the chief priests and the elders, he gave no answer.
13 Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
Then Pilate said to him, “Do yoʋ not hear all the things they are testifying against yoʋ?”
14 Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
But he gave him no answer, not even to a single charge, so the governor was greatly amazed.
15 To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
Now at the feast the governor was accustomed to release one prisoner for the crowd, whomever they wanted.
16 A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
At that time they had a notorious prisoner named Barabbas.
17 To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
So when the crowds were gathered together, Pilate said to them, “Whom do you want me to release for you? Barabbas, or Jesus, who is called Christ?”
18 Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
(For he knew they had handed Jesus over out of envy.)
19 Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
While Pilate was sitting on the judgment seat, his wife sent him this message: “Have nothing to do with that righteous man, for I have suffered a great deal today in a dream because of him.”
20 A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
But the chief priests and the elders persuaded the crowds to ask for Barabbas to be released and for Jesus to be executed.
21 Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
In response the governor said to them, “Which of the two do you want me to release for you?” They said, “Barabbas.”
22 Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
So Pilate said to them, “What then shall I do with Jesus, who is called Christ?” They all said to him, “Let him be crucified!”
23 Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
Then the governor said, “Why? What evil has he done?” But they cried out all the more, “Let him be crucified!”
24 Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
When Pilate saw that he was achieving nothing and that a riot was breaking out, he took water and washed his hands before the crowd, saying, “I am innocent of the blood of this righteous man. See to it yourselves.”
25 Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
All the people answered, “His blood be on us and on our children!”
26 Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
Then he released for them Barabbas, but he scourged Jesus and handed him over to be crucified.
27 Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
Then the governor's soldiers took Jesus with them into the governor's headquarters and gathered against him the entire cohort of soldiers.
28 Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
They stripped him and put a scarlet robe on him,
29 Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
and then twisted together a crown of thorns and put it on his head. They put a reed in his right hand, and kneeling before him, they mocked him, saying, “Hail, King of the Jews!”
30 Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
Then they spit on him, took the reed, and beat him repeatedly on his head.
31 Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
When they had finished mocking him, they stripped him of the robe and put his own garments back on him. Then they led him away to crucify him.
32 Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
As they went out, they found a Cyrenian man named Simon. They pressed him into service, forcing him to carry Jesus' cross.
33 Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
When they came to a place called Golgotha (which means, “Place of the Skull”),
34 Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
they gave Jesus sour wine to drink, mixed with gall. But when he tasted it, he refused to drink it.
35 Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
After crucifying him, they divided his garments among themselves by casting lots.
36 Suka kuma zauna suna kallonsa.
Then they sat down and kept watch over him there.
37 A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
Over his head they placed the written charge against him, which read, “This is Jesus, the King of the Jews.”
38 An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
Then two robbers were crucified with him, one on his right and one on his left.
39 Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
Those who passed by reviled him, shaking their heads
40 suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
and saying, “Yoʋ who would destroy the temple and build it in three days, save yoʋrself. If yoʋ are the Son of God, come down from the cross!”
41 Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
In the same way the chief priests also, along with the scribes, elders, and Pharisees, were mocking him, saying,
42 “Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
“He saved others, but he cannot save himself. If he is the king of Israel, let him come down now from the cross, and we will believe in him.
43 Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
He has put his trust in God; let God deliver him now if he wants him, for he said, ‘I am the Son of God.’”
44 Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
The robbers who were crucified with him were also reviling him in the same way.
45 To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
From the sixth hour until the ninth hour, there was darkness over the whole land.
46 Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
And about the ninth hour Jesus cried out with a loud voice, “Eli, Eli, lima sabachthani?” that is, “My God, my God, why have yoʋ forsaken me?”
47 Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
When some of those standing there heard this, they said, “This man is calling for Elijah.”
48 Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
Immediately one of them ran, got a sponge, filled it with sour wine, put it on a reed, and gave it to him to drink.
49 Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
But the rest said, “Leave him alone. Let us see if Elijah comes to save him.”
50 Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
Then Jesus cried out again with a loud voice and gave up his spirit.
51 Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
And behold, the veil of the temple was torn in two from top to bottom. The earth was shaken, and the rocks were split.
52 Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
The tombs were opened, and the bodies of many saints who had fallen asleep were raised.
53 Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
(They came out of the tombs, and after his resurrection they went into the holy city and appeared to many.)
54 Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
Now when the centurion and those who were keeping watch with him over Jesus saw the earthquake and the things that had happened, they became very frightened and said, “Truly this man was the Son of God.”
55 Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
Many women who had followed Jesus from Galilee and provided for him were there looking on from a distance,
56 A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
among whom were Mary Magdalene, Mary the mother of James and Joses, and the mother of the sons of Zebedee.
57 Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
When it was evening, there came a rich man from Arimathea named Joseph, who was himself also a disciple of Jesus.
58 Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
He went to Pilate and asked for Jesus' body. So Pilate commanded that the body be given to him.
59 Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
Joseph took the body, wrapped it in a clean linen cloth,
60 sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
and laid it in his own new tomb, which he had hewn in a rock. Then he rolled a large stone against the entrance of the tomb and went away.
61 Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
Mary Magdalene was there, and so was the other Mary, sitting across from the tomb.
62 Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
The next day (that is, after the day of Preparation), the chief priests and the Pharisees gathered together before Pilate
63 Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
and said, “Sir, we remember that while he was still alive that deceiver said, ‘After three days I will rise again.’
64 Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
Therefore command that the tomb be secured until the third day, lest his disciples come by night, steal him away, and say to the people, ‘He has been raised from the dead.’ This last deception would be worse than the first.”
65 Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
Pilate said to them, “You have a guard of soldiers. Go and make it as secure as you know how.”
66 Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.
So they went and secured the tomb by sealing the stone and posting the guard of soldiers.