< Mattiyu 25 >
1 Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
Thanne the kyngdoom of heuenes schal be lijk to ten virgyns, whiche token her laumpis, and wenten out ayens the hosebonde and the wijf;
2 Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
and fyue of hem weren foolis, and fyue prudent.
3 Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
But the fyue foolis token her laumpis, and token not oile with hem;
4 Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
but the prudent token oile in her vessels with the laumpis.
5 To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
And whilis the hosebonde tariede, alle thei nappiden and slepten.
6 Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
But at mydnyyt a cryy was maad, Lo! the spouse cometh, go ye oute to mete with him.
7 Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
Thanne alle tho virgyns risen vp, and araieden her laumpis.
8 Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
And the foolis seiden to the wise, Yyue ye to vs of youre oile, for oure laumpis ben quenchid.
9 “Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
The prudent answeriden, and seiden, Lest perauenture it suffice not to vs and to you, go ye rather to men that sellen, and bie to you.
10 Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
And while thei wenten for to bie, the spouse cam; and tho that weren redi, entreden with him to the weddyngis; and the yate was schit.
11 Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
And at the last the othere virgyns camen, and seiden, Lord, lord, opene to vs.
12 Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
And he answeride, and seide, Treuli Y seie to you, Y knowe you not.
13 Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
Therfor wake ye, for ye witen not the dai ne the our.
14 Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
For as a man that goith in pilgrimage, clepide hise seruauntis, and bitook to hem hise goodis;
15 Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
and to oon he yaf fyue talentis, and to another tweyne, and to another oon, to ech after his owne vertu; and wente forth anoon.
16 nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
And he that hadde fyue besauntis, wente forth, and wrouyte in hem, and wan othere fyue.
17 Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
Also and he that hadde takun tweyne, wan othere tweyne.
18 Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
But he that hadde takun oon, yede forth, and dalf in to the erthe, and hidde the money of his lord.
19 To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
But after long tyme, the lord of tho seruauntis cam, and rekenede with hem.
20 Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
And he that hadde takun fyue besauntis, cam, and brouyte othere fyue, and seide, Lord, thou bytokist to me fyue besauntis, loo! Y haue getun aboue fyue othere.
21 Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
His lord seide to hym, Wel be thou, good seruaunt and feithful; for on fewe thingis thou hast be trewe, Y schal ordeyne thee on manye thingis; entre thou in to the ioye of thi lord.
22 Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
And he that hadde takun twey talentis, cam, and seide, Lord, thou bitokist to me twey besauntis; loo!
23 Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
Y haue wonnen ouer othir tweyne. His lord seide to him, Wel be thou, good seruaunt and trewe; for on fewe thingis thou hast be trewe, Y schal ordeyne thee on many thingis; entre thou in to the ioie of thi lord.
24 Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
But he that hadde takun o besaunt, cam, and seide, Lord, Y woot that thou art an hard man; thou repist where thou hast not sowe, and thou gederist togidere where thou hast not spred abrood;
25 Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
and Y dredynge wente, and hidde thi besaunt in the erthe; lo! thou hast that that is thin.
26 Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
His lord answeride, and seide to hym, Yuel seruaunt and slowe, wistist thou that Y repe where Y sewe not, and gadir to gidere where Y spredde not abrood?
27 To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
Therfor it bihofte thee to bitake my money to chaungeris, that whanne Y cam, Y schulde resseyue that that is myn with vsuris.
28 Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
Therfor take awei fro hym the besaunt, and yyue ye to hym that hath ten besauntis.
29 Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
For to euery man that hath me schal yyue, and he schal encreese; but fro hym that hath not, also that that hym semeth to haue, schal be taken awey fro him.
30 Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
And caste ye out the vnprofitable seruaunt in to vtmer derknessis; ther schal be wepyng, and gryntyng of teeth.
31 Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
Whanne mannus sone schal come in his maieste, and alle hise aungels with hym, thanne he schal sitte on the sege of his maieste;
32 A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
and alle folkis schulen be gaderid bifor hym,
33 Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
and he schal departe hem atwynne, as a scheeperde departith scheep from kidis; and he schal sette the scheep on his riythalf, and the kidis on the lefthalf.
34 Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
Thanne the kyng schal seie to hem, that schulen be on his riythalf, Come ye, the blessid of my fadir, take ye in possessioun the kyngdoom maad redi to you fro the makyng of the world.
35 Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
For Y hungride, and ye yauen me to ete; Y thristide, and ye yauen me to drynke; Y was herboreles, and ye herboriden me;
36 Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
nakid, and ye hiliden me; sijk, and ye visitiden me; Y was in prisoun, and ye camen to me.
37 Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
Thanne iust men schulen answere to hym, and seie, Lord, whanne siyen we thee hungry, and we fedden thee; thristi, and we yauen to thee drynk?
38 Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
and whanne sayn we thee herborles, and we herboreden thee; or nakid, and we hiliden thee?
39 Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
or whanne sayn we thee sijk, or in prisoun, and we camen to thee?
40 Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
And the kyng answerynge schal seie to hem, Treuli Y seie to you, as longe as ye diden to oon of these my leeste britheren, ye diden to me.
41 Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios , questioned)
Thanne the kyng schal seie also to hem, that schulen be on his lefthalf, Departe fro me, ye cursid, in to euerlastynge fijr, that is maad redi to the deuel and hise aungels. (aiōnios )
42 domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
For Y hungride, and ye yauen not me to ete; Y thristide, and ye yauen not me to drynke;
43 Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
Y was herborles, and ye herberden not me; nakid, and ye keuerden not me; sijk, and in prisoun, and ye visitiden not me.
44 Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
Thanne and thei schulen answere to hym, and schulen seie, Lord, whanne sayn we thee hungrynge, or thristynge, or herboreles, or nakid, or sijk, or in prisoun, and we serueden not to thee?
45 Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
Thanne he schal answere to hem, and seie, Treuli Y seie to you, `hou longe ye diden not to oon of these leeste, nether ye diden to me.
46 Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios )
And these schulen goo in to euerlastynge turment; but the iust men schulen go in to euerlastynge lijf. (aiōnios )