< Mattiyu 25 >

1 Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
Then shall the kingdom of heaven be likened to ten virgins, which took their lamps, and went forth to meet the bridegroom.
2 Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
And five of them were wise, and five were foolish.
3 Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
They that were foolish took their lamps, and took no oil with them:
4 Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
But the wise took oil in their vessels with their lamps.
5 To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
While the bridegroom tarried, they all slumbered and slept.
6 Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
And at midnight there was a cry made, Behold, the bridegroom comes; go you out to meet him.
7 Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
Then all those virgins arose, and trimmed their lamps.
8 Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
And the foolish said to the wise, Give us of your oil; for our lamps are gone out.
9 “Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
But the wise answered, saying, Not so; lest there be not enough for us and you: but go you rather to them that sell, and buy for yourselves.
10 Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
And while they went to buy, the bridegroom came; and they that were ready went in with him to the marriage: and the door was shut.
11 Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
Afterward came also the other virgins, saying, Lord, Lord, open to us.
12 Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
But he answered and said, Truly I say to you, I know you not.
13 Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
Watch therefore, for you know neither the day nor the hour wherein the Son of man comes.
14 Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
For the kingdom of heaven is as a man traveling into a far country, who called his own servants, and delivered to them his goods.
15 Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
And to one he gave five talents, to another two, and to another one; to every man according to his several ability; and straightway took his journey.
16 nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
Then he that had received the five talents went and traded with the same, and made them other five talents.
17 Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
And likewise he that had received two, he also gained other two.
18 Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
But he that had received one went and dig in the earth, and hid his lord’s money.
19 To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
After a long time the lord of those servants comes, and reckons with them.
20 Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
And so he that had received five talents came and brought other five talents, saying, Lord, you delivered to me five talents: behold, I have gained beside them five talents more.
21 Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
His lord said to him, Well done, you good and faithful servant: you have been faithful over a few things, I will make you ruler over many things: enter you into the joy of your lord.
22 Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
He also that had received two talents came and said, Lord, you delivered to me two talents: behold, I have gained two other talents beside them.
23 Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
His lord said to him, Well done, good and faithful servant; you have been faithful over a few things, I will make you ruler over many things: enter you into the joy of your lord.
24 Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
Then he which had received the one talent came and said, Lord, I knew you that you are an hard man, reaping where you have not sown, and gathering where you have not strewed:
25 Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
And I was afraid, and went and hid your talent in the earth: see, there you have that is yours.
26 Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
His lord answered and said to him, You wicked and slothful servant, you knew that I reap where I sowed not, and gather where I have not strewed:
27 To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
You should therefore to have put my money to the exchangers, and then at my coming I should have received my own with usury.
28 Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
Take therefore the talent from him, and give it to him which has ten talents.
29 Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
For to every one that has shall be given, and he shall have abundance: but from him that has not shall be taken away even that which he has.
30 Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
And cast you the unprofitable servant into outer darkness: there shall be weeping and gnashing of teeth.
31 Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
When the Son of man shall come in his glory, and all the holy angels with him, then shall he sit on the throne of his glory:
32 A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
And before him shall be gathered all nations: and he shall separate them one from another, as a shepherd divides his sheep from the goats:
33 Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
And he shall set the sheep on his right hand, but the goats on the left.
34 Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
Then shall the King say to them on his right hand, Come, you blessed of my Father, inherit the kingdom prepared for you from the foundation of the world:
35 Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
For I was an hungered, and you gave me meat: I was thirsty, and you gave me drink: I was a stranger, and you took me in:
36 Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
Naked, and you clothed me: I was sick, and you visited me: I was in prison, and you came to me.
37 Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
Then shall the righteous answer him, saying, Lord, when saw we you an hungered, and fed you? or thirsty, and gave you drink?
38 Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
When saw we you a stranger, and took you in? or naked, and clothed you?
39 Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
Or when saw we you sick, or in prison, and came to you?
40 Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
And the King shall answer and say to them, Truly I say to you, Inasmuch as you have done it to one of the least of these my brothers, you have done it to me.
41 Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios g166, questioned)
Then shall he say also to them on the left hand, Depart from me, you cursed, into everlasting fire, prepared for the devil and his angels: (aiōnios g166)
42 domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
For I was an hungered, and you gave me no meat: I was thirsty, and you gave me no drink:
43 Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
I was a stranger, and you took me not in: naked, and you clothed me not: sick, and in prison, and you visited me not.
44 Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
Then shall they also answer him, saying, Lord, when saw we you an hungered, or thirsty, or a stranger, or naked, or sick, or in prison, and did not minister to you?
45 Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
Then shall he answer them, saying, Truly I say to you, Inasmuch as you did it not to one of the least of these, you did it not to me.
46 Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios g166)
And these shall go away into everlasting punishment: but the righteous into life eternal. (aiōnios g166)

< Mattiyu 25 >