< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
Comme Jésus s’en allait, au sortir du temple, ses disciples s’approchèrent pour lui en faire remarquer les constructions.
2 Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
Mais il leur dit: Voyez-vous tout cela? Je vous le dis en vérité, il ne restera pas ici pierre sur pierre qui ne soit renversée.
3 Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn )
Il s’assit sur la montagne des oliviers. Et les disciples vinrent en particulier lui faire cette question: Dis-nous, quand cela arrivera-t-il, et quel sera le signe de ton avènement et de la fin du monde? (aiōn )
4 Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
Jésus leur répondit: Prenez garde que personne ne vous séduise.
5 Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
Car plusieurs viendront sous mon nom, disant: C’est moi qui suis le Christ. Et ils séduiront beaucoup de gens.
6 Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
Vous entendrez parler de guerres et de bruits de guerres: gardez-vous d’être troublés, car il faut que ces choses arrivent. Mais ce ne sera pas encore la fin.
7 Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
Une nation s’élèvera contre une nation, et un royaume contre un royaume, et il y aura, en divers lieux, des famines et des tremblements de terre.
8 Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
Tout cela ne sera que le commencement des douleurs.
9 Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
Alors on vous livrera aux tourments, et l’on vous fera mourir; et vous serez haïs de toutes les nations, à cause de mon nom.
10 Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
Alors aussi plusieurs succomberont, et ils se trahiront, se haïront les uns les autres.
11 Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
Plusieurs faux prophètes s’élèveront, et ils séduiront beaucoup de gens.
12 Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
Et, parce que l’iniquité se sera accrue, la charité du plus grand nombre se refroidira.
13 Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
Mais celui qui persévérera jusqu’à la fin sera sauvé.
14 Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
Cette bonne nouvelle du royaume sera prêchée dans le monde entier, pour servir de témoignage à toutes les nations. Alors viendra la fin.
15 Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
C’est pourquoi, lorsque vous verrez l’abomination de la désolation, dont a parlé le prophèteDaniel, établie en lieu saint, que celui qui lit fasse attention!
16 bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
alors, que ceux qui seront en Judée fuient dans les montagnes;
17 Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
que celui qui sera sur le toit ne descende pas pour prendre ce qui est dans sa maison;
18 kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
et que celui qui sera dans les champs ne retourne pas en arrière pour prendre son manteau.
19 Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
Malheur aux femmes qui seront enceintes et à celles qui allaiteront en ces jours-là!
20 Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
Priez pour que votre fuite n’arrive pas en hiver, ni un jour desabbat.
21 Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
Car alors, la détresse sera si grande qu’il n’y en a point eu de pareille depuis le commencement du monde jusqu’à présent, et qu’il n’y en aura jamais.
22 In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
Et, si ces jours n’étaient abrégés, personne ne serait sauvé; mais, à cause des élus, ces jours seront abrégés.
23 Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
Si quelqu’un vous dit alors: Le Christ est ici, ou: Il est là, ne le croyez pas.
24 Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
Car il s’élèvera de faux Christs et de faux prophètes; ils feront de grands prodiges et des miracles, au point de séduire, s’il était possible, même les élus.
25 Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
Voici, je vous l’ai annoncé d’avance.
26 Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
Si donc on vous dit: Voici, il est dans le désert, n’y allez pas; voici, il est dans les chambres, ne le croyez pas.
27 Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
Car, comme l’éclair part de l’orient et se montre jusqu’en occident, ainsi sera l’avènement du Fils de l’homme.
28 Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
En quelque lieu que soit le cadavre, là s’assembleront les aigles.
29 Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
Aussitôt après ces jours de détresse, le soleil s’obscurcira, la lune ne donnera plus sa lumière, les étoiles tomberont du ciel, et les puissances des cieux seront ébranlées.
30 Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Alors le signe du Fils de l’homme paraîtra dans le ciel, toutes les tribus de la terrese lamenteront, et elles verront le Fils de l’homme venant sur les nuées du ciel avec puissance et une grande gloire.
31 Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
Il enverra ses anges avecla trompette retentissante, et ils rassembleront ses élus des quatre vents, depuis une extrémité des cieux jusqu’à l’autre.
32 Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
Instruisez-vous par une comparaison tirée du figuier. Dès que ses branches deviennent tendres, et que les feuilles poussent, vous connaissez que l’été est proche.
33 Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
De même, quand vous verrez toutes ces choses, sachez que le Fils de l’homme est proche, à la porte.
34 Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
Je vous le dis en vérité, cette génération ne passera point, que tout cela n’arrive.
35 Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
36 Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
Pour ce qui est du jour et de l’heure, personne ne le sait, ni les anges des cieux, ni le Fils, mais le Père seul.
37 Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
Ce qui arriva du temps de Noé arrivera de même à l’avènement du Fils de l’homme.
38 A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
Car, dans les jours qui précédèrent le déluge, les hommes mangeaient et buvaient, se mariaient et mariaient leurs enfants, jusqu’au jour où Noé entra dans l’arche;
39 ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
et ils ne se doutèrent de rien, jusqu’à ce que le déluge vînt et les emportât tous: il en sera de même à l’avènement du Fils de l’homme.
40 Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
Alors, de deux hommes qui seront dans un champ, l’un sera pris et l’autre laissé;
41 Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
de deux femmes qui moudront à la meule, l’une sera prise et l’autre laissée.
42 Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
Veillez donc, puisque vous ne savez pas quel jour votre Seigneur viendra.
43 Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
Sachez-le bien, si le maître de la maison savait à quelle veille de la nuit le voleur doit venir, il veillerait et ne laisserait pas percer sa maison.
44 Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
C’est pourquoi, vous aussi, tenez-vous prêts, car le Fils de l’homme viendra à l’heure où vous n’y penserez pas.
45 To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
Quel est donc le serviteur fidèle et prudent, que son maître a établi sur ses gens, pour leur donner la nourriture au temps convenable?
46 Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
Heureux ce serviteur, que son maître, à son arrivée, trouvera faisant ainsi!
47 Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
Je vous le dis en vérité, il l’établira sur tous ses biens.
48 Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
Mais, si c’est un méchant serviteur, qui dise en lui-même: Mon maître tarde à venir,
49 sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
s’il se met à battre ses compagnons, s’il mange et boit avec les ivrognes,
50 uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
le maître de ce serviteur viendra le jour où il ne s’y attend pas et à l’heure qu’il ne connaît pas,
51 Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
il le mettra en pièces, et lui donnera sa part avec les hypocrites: c’est là qu’il y aura des pleurs et des grincements de dents.