< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
Og Jesus gik ud, bort fra Helligdommen, og hans Disciple kom til ham for at vise ham Helligdommens Bygninger.
2 Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
Men han svarede og sagde til dem: "Se I ikke alt dette? Sandelig, siger jeg eder, her skal ikke lades Sten på Sten, som jo skal nedbrydes."
3 Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?” (aiōn )
Men da han sad på Oliebjerget, kom hans Disciple til ham afsides og sagde: "Sig os, når skal dette ske? Og hvad er Tegnet på din Tilkommelse og Verdens Ende?" (aiōn )
4 Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
Og Jesus svarede og sagde til dem: "Ser til, at ingen forfører eder!
5 Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
Thi mange skulle på mit Navn komme og sige: Jeg er Kristus; og de skulle forføre mange.
6 Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
Men I skulle få at høre om Krige og Krigsrygter. Ser til, lader eder ikke forskrække; thi det må ske; men Enden er ikke endda.
7 Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
Thi Folk skal rejse sig mod Folk, og Rige mod Rige, og der skal være Hungersnød og Jordskælv her og der.
8 Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
Men alt dette er Veernes Begyndelse.
9 Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
Da skulle de overgive eder til Trængsel og slå eder ihjel, og I skulle hades af alle Folkeslagene for mit Navns Skyld.
10 Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
Og da skulle mange forarges og forråde hverandre og hade hverandre.
11 Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
Og mange falske Profeter skulle fremstå og forføre mange.
12 Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
Og fordi Lovløsheden bliver mangfoldig, vil Kærligheden blive kold hos de fleste.
13 Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
Men den, som holder ud indtil Enden, han skal frelses.
14 Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
Og dette Rigets Evangelium skal prædikes i hele Verden til et Vidnesbyrd for alle Folkeslagene; og da skal Enden komme.
15 Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
Når I da se Ødelæggelsens Vederstyggelighed, hvorom der er talt ved Profeten Daniel, stå på hellig Grund, (den, som læser det, han give Agt!)
16 bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
da skulle de, som ere i Judæa, fly ud på Bjergene;
17 Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
den, som er på Taget, stige ikke ned for at hente, hvad der er i hans Hus;
18 kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
og den, som er på Marken, vende ikke tilbage før at hente sine Klæder!
19 Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
Men ve de frugtsommelige og dem, som give Die, i de Dage!
20 Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
Og beder om, at eders Flugt ikke skal ske om Vinteren, ej heller på en Sabbat;
21 Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
thi der skal da være en Trængsel så stor, som der ikke har været fra Verdens Begyndelse indtil nu og heller ikke skal komme.
22 In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
Og dersom disse Dage ikke bleve afkortede, da blev intet Kød frelst; men for de udvalgtes Skyld skulle disse Dage afkortes.
23 Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
Dersom nogen da siger til eder: Se, her er Kristus, eller der! da skulle I ikke tro det.
24 Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
Thi falske Krister og falske Profeter skulle fremstå og gøre store Tegn og Undergerninger, så at også de udvalgte skulde blive forførte, om det var muligt.
25 Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
Se, jeg har sagt eder det forud.
26 Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
Derfor, om de sige til eder: Se, han er i Ørkenen, da går ikke derud; se. han er i Kamrene, da tror det ikke!
27 Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
Thi ligesom Lynet udgår fra Østen og lyser indtil Vesten, således skal Menneskesønnens Tilkommelse være.
28 Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
Hvor Ådselet er, der ville Ørnene samle sig.
29 Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
Men straks efter de Dages Trængsel skal Solen formørkes og Månen ikke give sit Skin og Stjernerne falde ned fra Himmelen, og Himmelens Kræfter skulle rystes.
30 Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Og da skal Menneskesønnens Tegn vise sig på Himmelen; og da skulle alle Jordens Stammer jamre sig, og de skulle se Menneskesønnen komme på Himmelens Skyer med Kraft og megen Herlighed.
31 Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
Og han skal udsende sine Engle med stærktlydende Basun, og de skulle samle hans udvalgte fra de fire Vinde, fra den ene Ende af Himmelen til den anden.
32 Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
Men lærer Lignelsen af Figentræet: Når dets Gren allerede er bleven blød, og Bladene skyde frem, da skønne I, at Sommeren er nær.
33 Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
Således skulle også I, når I se alt dette, skønne, at han er nær for Døren.
34 Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
Sandelig, siger jeg eder, denne Slægt skal ingenlunde forgå, førend alle disse Ting ere skete.
35 Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
Himmelen og Jorden skulle forgå, men mine Ord skulle ingenlunde forgå.
36 Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
Men om den Dag og Time ved ingen, end ikke Himmelens Engle, heller ikke Sønnen, men kun Faderen alene.
37 Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
Og ligesom Noas dage vare, således skal Menneskesønnens Tilkommelse være.
38 A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
Thi ligesom de i Dagene før Syndfloden åde og drak, toge til Ægte og bortgiftede, indtil den Dag, da Noa gik ind i Arken,
39 ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
og ikke agtede det, førend Syndfloden kom og tog dem alle bort, således skal også Menneskesønnens Tilkommelse være.
40 Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
Da skulle to Mænd være på Marken; den ene tages med, og den anden lades tilbage.
41 Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
To Kvinder skulle male på Kværnen; den ene tages med, og den anden lades tilbage.
42 Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
Våger derfor, thi I vide ikke, på hvilken Dag eders Herre kommer.
43 Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
Men dette skulle I vide, at dersom Husbonden vidste. i hvilken Nattevagt Tyven vilde komme, da vågede han og tillod ikke, at der skete Indbrud i hans Hus.
44 Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
Derfor vorder også I rede; thi Menneskesønnen kommer i den Time, som I ikke mene.
45 To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
Hvem er så den tro og forstandige Tjener, som hans Herre har sat over sit Tyende til at give dem deres Mad i rette Tid?
46 Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
Salig er den Tjener, hvem hans Herre, når han kommer, finder handlende således.
47 Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
Sandelig, siger jeg eder, han skal sætte ham over alt, hvad han ejer.
48 Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
Men dersom den onde Tjener siger i sit Hjerte: Min Herre tøver,
49 sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
og så begynder at slå sine Medtjenere og spiser og drikker med Drankerne,
50 uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
da skal den Tjeners Herre komme på den Dag, han ikke venter, og i den Time, han ikke ved,
51 Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
og hugge ham sønder og give ham hans Lod sammen med Hyklerne; der skal der være Gråd og Tænders Gnidsel.