< Mattiyu 23 >

1 Sai Yesu yayi wa taron da alamajiransa magana.
Then Jesus spoke to the multitude, and to his disciples,
2 Ya ce, “Marubuta da Farisawa suna zaune a mazaunin Musa.
Saying, The scribes and the Pharisees sit in Moses's seat.
3 Don haka, duk abinda suka umarceku kuyi, kuyi wadannan abubuwa ku kuma kiyaye su. Amma kada kuyi koyi da ayyukansu, gama suna fadar abubuwa amma kuma ba su aikata su.
All therefore, whatever they bid you observe, [that] observe and do: but do not ye according to their works: for they say, and do not.
4 I, sukan daura kaya masu nauyi, masu wuyar dauka, daga nan su dauka su jibga wa mutane a kafada. Amma su kan su baza su mika danyatsa ba su dauka.
For they bind heavy burdens, and grievous to be borne, and lay [them] on men's shoulders; but they [themselves] will not move them with one of their fingers.
5 Duk ayyukan su suna yi ne don mutane su gani, suna dinka aljihunan nassinsu da fadi, suna fadada iyakokin rigunansu.
But all their works they do to be seen by men: they make broad their phylacteries, and enlarge the borders of their garments,
6 Su na son mafifitan wuraren zama a gidan biki, da mafifitan wuraren zama a majami'u,
And love the uppermost rooms at feasts, and the chief seats in the synagogues,
7 da kuma gaisuwar musamman a wuraren kasuwanci, a kuma rika ce da su 'mallam.'
And greetings in the markets, and to be called by men, Rabbi, Rabbi.
8 Amma ba sai an kira ku 'mallam, ba' domin malami daya kuke da shi, ku duka kuwa 'yan'uwan juna ne.
But be not ye called Rabbi: for one is your Master, [even] Christ; and all ye are brethren.
9 Kada ku kira kowa 'Ubanku' a duniya, domin Uba daya ne ku ke da shi, kuma yana sama.
And call no [man] your father upon the earth: for one is your Father who is in heaven.
10 Kada kuma a kira ku malamai, saboda malamin ku daya ne, shi ne Almasihu.
Neither be ye called masters: for one is your master, [even] Christ.
11 Amma wanda yake babba a cikin ku zaya zama bawanku.
But he that is greatest among you, shall be your servant.
12 Duk wanda ya daukaka kansa za a kaskantar dashi. Duk wanda ya kaskantar da kansa kuma za a daukaka shi.
And whoever shall exalt himself, shall be abased; and he that shall humble himself, shall be exalted.
13 Amma kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kun toshewa mutane kofar mulkin sama. Baku shiga ba, kuma ba ku bar wadanda suke so su sami shiga ba.
But woe to you, scribes and Pharisees! hypocrites! for ye shut up the kingdom of heaven against men: for ye neither go in [yourselves], neither suffer ye them that are entering, to go in.
14 kaiton ku marubuta da Farisawa, domin kuna hallaka gwauraya -
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye devour widows' houses, and for a pretense make long prayer: therefore ye shall receive the greater damnation.
15 Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kuna tafiya ketaren tekuna da kasashe domin samun almajiri daya tak, in kwa kun samu kukan mai da shi biyunku danwuta. (Geenna g1067)
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye compass sea and land to make one proselyte, and when he is made, ye make him two-fold more the child of hell than yourselves. (Geenna g1067)
16 Kaiton ku, makafin jagora, kuda kuke cewa, Kowa ya rantse da Haikali, ba komai. Amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, rantsuwarsa ta daure shi.'
Woe to you, [ye] blind guides, who say, Whoever shall swear by the temple, it is nothing; but whoever shall swear by the gold of the temple, he is a debtor.
17 Ku wawayen makafi! wanene yafi girma, zinariyar ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar?
[Ye] fools, and blind: for which is greater, the gold, or the temple that sanctifieth the gold?
18 Kuma, 'Kowa ya rantse da bagadi, ba komai bane. Amma duk wanda ya rantse da baikon da aka dora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.'
And whoever shall swear by the altar, it is nothing; but whoever sweareth by the gift that is upon it, he is guilty.
19 Ku makafi! Wanene yafi girma, baikon ko kuwa bagadin da yake kebe baikon ga Allah?
[Ye] fools, and blind: for which [is] greater, the gift, or the altar that sanctifieth the gift?
20 Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagadi, ya rantse da shi da duk abinda ke kansa.
Whoever therefore shall swear by the altar, sweareth by it, and by all things upon it.
21 Kuma duk wanda ya rantse da Haikali ya rantse dashi da kuma wanda yake cikin sa.
And whoever shall swear by the temple, sweareth by it, and by him that dwelleth in it.
22 Kuma duk wanda ya rantse da sama, ya rantse da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune akai.
And he that shall swear by heaven, sweareth by the throne of God, and by him that sitteth upon it.
23 Kaiton ku Farisawa da marubuta, munafukai! Kukan fitar da zakkar doddoya, da karkashi, da lamsur, amma kun yar da al'amuran attaura mafi nauyi-, wato, hukunci, da jinkai da bangaskiya. Wadannan ne ya kamata kuyi, ba tare da kunyi watsi da sauran ba.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye pay tithe of mint, and anise, and cummin, and have omitted the weightier [matters] of the law, judgment, mercy, and faith: these ye ought to have done, and not to leave the others undone.
24 Makafin jagora, ku kan burtsar da kwaro dan mitsil, amma kukan hadiye rakumi!
[Ye] blind guides, who strain out a gnat, and swallow a camel.
25 Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! kuna wanke bayan moda da kwano, amma aciki cike suke da zalunci da keta.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye make clean the outside of the cup and of the platter, but within they are full of extortion and excess.
26 Kai makahon Bafarise! Sai ka fara tsarkake cikin modar da kwanon domin bayansu ma su tsarkaka.
[Thou] blind Pharisee, cleanse first that [which is] within the cup and platter, that the outside of them may be clean also.
27 Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar kasa kuke, masu kyaun gani daga waje, daga ciki kuwa sai kasusuwan matattu da kazanta iri iri.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye are like whitened sepulchers, which indeed appear beautiful outward, but are within full of dead [men's] bones, and of all uncleanness.
28 Haka nan kuke a idanun mutane ku adalai ne, amma a ciki sai munafunci da mugun aiki.
Thus ye also outwardly appear righteous to men, but within ye are full of hypocrisy and iniquity.
29 Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Ku kan gina kaburburan annabawa, kuna kuma kawata kaburburan adalai.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! because ye build the tombs of the prophets, and garnish the sepulchers of the righteous,
30 Kuna cewa, 'Da muna nan a zamanin Ubanninmu, da bamu basu goyon baya ba wajen zubar da jinin annabawa.'
And say, If we had been in the days of our fathers, we would not have been partakers with them in the blood of the prophets.
31 Domin haka kun shaida kanku ku ne 'ya'yan masu kisan annabawa.
Wherefore ye are witnesses to yourselves, that ye are the children of them who killed the prophets.
32 Sai kuma kuka cika ma'aunin ubanninku!
Fill ye up then the measure of your fathers.
33 macizai, Ku 'ya'yan ganshekai, Yaya zaku tsere wa hukuncin Gidan wuta? (Geenna g1067)
[Ye] serpents, [ye] generation of vipers, how can ye escape the damnation of hell? (Geenna g1067)
34 Saboda haka, duba, ina aiko maku da annabawa, da masu hikima da marubuta. Za ku kashe wadansun su kuma ku gicciye su. Zaku yiwa wasu bulala a majami'un ku, kuna bin su gari gari.
Wherefore behold, I send to you prophets, and wise men, and scribes; and [some] of them ye will kill and crucify, and [some] of them ye will scourge in your synagogues, and persecute [them] from city to city:
35 Sakamakon hakan alhakin jinin dukkan adalai da aka zubar a duniya ya komo a kan ku, tun daga jinin Habila adali har ya zuwa na Zakariya dan Barakiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikali da bagadi.
That upon you may come all the righteous blood shed upon the earth, from the blood of righteous Abel, to the blood of Zacharias son of Barachias, whom ye slew between the temple and the altar.
36 Hakika, Ina gaya maku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.
Verily I say to you, all these things shall come upon this generation.
37 Urushalima, Urushalima, keda kika kashe annabawa kika kuma jejjefi wadanda aka turo maki da duwatsu! Sau nawa ne naso in tattaro ki kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta cikin fukafukanta, amma kin ki.
O Jerusalem, Jerusalem, [thou] that killest the prophets, and stonest them who are sent to thee, how often would I have gathered thy children, even as a hen gathereth her chickens under [her] wings, and ye would not!
38 Ga shi an bar maku gidan ku a yashe!
Behold, your house is left to you desolate.
39 Ina dai gaya maku, ba za ku kara gani na ba, sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.”'
For I say to you, Ye shall not see me henceforth, till ye shall say, Blessed [is] he that cometh in the name of the Lord.

< Mattiyu 23 >