< Mattiyu 22 >
1 Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
Alors Jésus prenant la parole, leur parla encore par similitudes, disant:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
Le Royaume des cieux est semblable à un Roi qui fit les noces de son fils.
3 Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
Et il envoya ses serviteurs pour appeler ceux qui avaient été conviés aux noces; mais ils n'y voulurent point venir.
4 Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
Il envoya encore d'autres serviteurs, disant: dites à ceux qui étaient conviés: voici, j'ai apprêté mon dîner; mes taureaux et mes bêtes grasses sont tuées, et tout est prêt; venez aux noces.
5 Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
Mais eux n'en tenant point de compte, s'en allèrent l'un à sa métairie, et l'autre à son trafic.
6 Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
Et les autres prirent ses serviteurs, et les outragèrent, et les tuèrent.
7 Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
Quand le Roi l'entendit, il se mit en colère, et y ayant envoyé ses troupes, il fit périr ces meurtriers-là, et brûla leur ville.
8 Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
Puis il dit à ses serviteurs: Eh bien! les noces sont apprêtées, mais ceux qui y étaient conviés n'en étaient pas dignes.
9 Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
Allez donc aux carrefours des chemins, et autant de gens que vous trouverez, conviez-les aux noces.
10 Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
Alors ses serviteurs allèrent dans les chemins, et assemblèrent tous ceux qu'ils trouvèrent, tant mauvais que bons, tellement que le lieu des noces fut rempli de gens qui étaient à table.
11 Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
Et le Roi étant entré pour voir ceux qui étaient à table, il y vit un homme qui n'était pas vêtu d'une robe de noces.
12 Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
Et il lui dit: mon ami, comment es-tu entré ici, sans avoir une robe de noces? et il eut la bouche fermée.
13 Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
Alors le Roi dit aux serviteurs: liez-le pieds et mains, emportez-le, et le jetez dans les ténèbres de dehors; là il y aura des pleurs et des grincements de dents.
14 Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
Car il y a beaucoup d'appelés, mais peu d'élus.
15 Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
Alors les Pharisiens s'étant retirés, consultèrent ensemble comment ils le surprendraient en paroles;
16 Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
Et ils lui envoyèrent leurs disciples, avec des Hérodiens, en disant: Maître, nous savons que tu es véritable, que tu enseignes la voie de Dieu en vérité, et que tu ne te soucies de personne; car tu ne regardes point à l'apparence des hommes.
17 To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
Dis-nous donc ce qu'il te semble de ceci: est-il permis de payer le tribut à César, ou non?
18 Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
Et Jésus connaissant leur malice, dit: Hypocrites, pourquoi me tentez-vous?
19 Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
Montrez-moi la monnaie de tribut; et ils lui présentèrent un denier.
20 Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
Et il leur dit: de qui est cette image, et cette inscription?
21 Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
Ils lui répondirent: de César. Alors il leur dit: rendez donc à César les choses qui sont à César, et à Dieu, celles qui sont à Dieu.
22 Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
Et ayant entendu cela ils en furent étonnés, et le laissant, ils s'en allèrent.
23 A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
Le même jour les Saducéens, qui disent qu'il n'y a point de résurrection, vinrent à lui, et l'interrogèrent,
24 cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
En disant: Maître, Moïse a dit: si quelqu'un vient à mourir sans enfants, que son frère prenne sa femme, et il donnera des enfants à son frère.
25 Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
Or il y avait parmi nous sept frères, dont l'aîné, après s'être marié, mourut, et n'ayant point eu d'enfants, laissa sa femme à son frère.
26 Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
De même le second, puis le troisième, jusques au septième.
27 Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
Et après eux tous, la femme mourut aussi.
28 To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
En la résurrection donc duquel des sept sera-t-elle femme? car tous l'ont eue.
29 Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
Mais Jésus répondant leur dit: vous errez, ne connaissant point les Ecritures, ni la puissance de Dieu.
30 Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
Car en la résurrection on ne prend ni on ne donne point de femmes en mariage, mais on est comme les Anges de Dieu dans le ciel.
31 Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
Et quant à la résurrection des morts, n'avez-vous point lu ce dont Dieu vous a parlé, disant:
32 'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
Je suis le Dieu d'Abraham, et le Dieu d'Isaac, et le Dieu de Jacob; [or] Dieu n'est pas le Dieu des morts, mais des vivants.
33 Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
Ce que les troupes ayant entendu, elles admirèrent sa doctrine.
34 Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
Et quand les Pharisiens eurent appris qu'il avait fermé la bouche aux Saducéens, ils s'assemblèrent dans un même lieu.
35 Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
Et l'un d'eux, qui était Docteur de la Loi, l'interrogea pour l'éprouver, en disant:
36 “Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
Maître, lequel est le grand commandement de la Loi?
37 Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
Jésus lui dit: tu aimeras le Seigneur ton Dieu de tout ton cœur, et de toute ton âme, et de toute ta pensée.
38 Wannan itace babbar doka ta farko.
Celui-ci est le premier et le grand commandement.
39 Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
Et le second semblable à celui-là, est: tu aimeras ton prochain comme toi-même.
40 Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
De ces deux commandements dépendent toute la Loi et les Prophètes.
41 Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
Et les Pharisiens étant assemblés, Jésus les interrogea,
42 Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
Disant: que vous semble-t-il du Christ? De qui est-il Fils? Ils lui répondirent: de David.
43 Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
Et il leur dit: comment donc David, [parlant] par l'Esprit, l'appelle-t-il [son] Seigneur? disant:
44 “Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
Le Seigneur a dit à mon Seigneur, assieds-toi à ma droite, jusqu'à ce que j'aie mis tes ennemis pour le marchepied de tes pieds.
45 Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
Si donc David l'appelle [son] Seigneur, comment est-il son Fils?
46 Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.
Et personne ne lui pouvait répondre un seul mot, ni personne n'osa plus l'interroger depuis ce jour-là.