< Mattiyu 20 >
1 Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa.
Sest taevariik on nagu maaomanik, kes läks varahommikul välja, et palgata töölisi oma viinamarjaistandusse.
2 Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.
Ta leppis töölistega kokku, et tasub päeva eest ühe denaari, ning saatis nad viinapuuaeda.
3 Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki.
Umbes kella üheksa ajal hommikul läks ta välja ja nägi teisi ilma tööta turuplatsil seismas.
4 Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.
„Minge ka teie viinamarjaistandusse tööle ja ma tasun teile, mis on sobiv, “ütles ta neile. Nii läksid ka nemad tööle.
5 Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din.
Keskpäeva ajal ja kella kolme ajal pärastlõunal läks ta välja ja toimis samamoodi.
6 Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?'
Kella viie ajal pärastlõunal läks ta välja ja leidis sealt veel inimesi seismas. „Miks te seisate siin kogu päeva ega tee midagi?“küsis ta neilt.
7 Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.
„Sest keegi ei ole meid palganud, “vastasid nad. „Minge ka viinamarjaistandusse tööle, “ütles ta neile.
8 Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.'
Kui saabus õhtu, ütles viinamarjaistanduse omanik töödejuhatajale: „Kutsu töötajad ja maksa neile palk. Alusta töölistest, kes palgati viimasena, ja seejärel liigu edasi nendeni, kes palgati esimesena.“
9 Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini.
Kui tulid need, kes oldi palgatud kella viie ajal pärastlõunal, said nad igaüks ühe denaari.
10 Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.
Kui siis tulid need, kes olid esimesena palgatud, arvasid nad, et nemad saavad rohkem, kuid ka nemad said ühe denaari.
11 Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar.
Kui nad said palga kätte, läksid nad omanikule kaebama.
12 Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'
„Need, kes viimasena palgati, töötasid ainult tund aega ja sa maksid neile sama palga nagu meile, kes me töötasime kogu päeva kõrvetavas kuumuses, “nurisesid nad.
13 Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba?
Omanik vastas ühele neist: „Mu sõber, ma ei ole sind ebaõiglaselt kohelnud. Kas sa ei leppinud minuga kokku, et töötad ühe denaari eest?
14 Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.
Võta oma palk ja mine. Ma tahan maksta viimasena palgatutele sama palju palka kui sulle.
15 Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?'
Kas ma ei või otsustada teha oma rahaga seda, mida tahan? Miks sa heidad mulle kurje pilke sellepärast, et ma tahan teha head?“
16 Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe.'' [An kira dayawa, amma kadan ne zababbu].
Nii saavad viimased esimesteks ja esimesed viimasteks.“
17 Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu,
Teel Jeruusalemma viis Jeesus kaksteist jüngrit kõndimise ajal kõrvale ja rääkis neile:
18 “Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa,
„Vaadake, me läheme Jeruusalemma ja inimese Poeg müüakse maha ülempreestritele ja vaimulikele õpetajatele. Nad mõistavad ta surma
19 za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi.''
ning annavad ta võõramaalaste kätte ja teda pilgatakse, piitsutatakse ja lüüakse risti. Kuid kolmandal päeval äratatakse ta surnuist üles.“
20 Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa.
Siis tuli Sebedeuse poegade ema koos oma kahe pojaga Jeesuse juurde. Ta põlvitas Jeesuse ette, et talle palve esitada.
21 Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?'' Sai ta ce masa, ''Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.
„Mis see on, mida sa minult palud?“küsis Jeesus temalt. „Palun määra nii, et mu pojad istuksid sinu kuningriigis sinu kõrval, üks sinu paremal ja teine sinu vasakul käel, “palus naine.
22 Amma Yesu ya amsa, ya ce, ''Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?'' Sai suka ce masa, ''Zamu iya.''
„Te ei tea, mida te palute, “ütles Jeesus neile. „Kas te olete võimelised jooma karikast, millest mina jooma hakkan?“„Jah, me oleme võimelised seda tegema, “vastasid nad talle.
23 Sai ya ce masu, ''In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne.''
„Te joote kindlasti minu karikast, “kostis ta neile, „kuid eesõigus minu paremal või vasakul käel istuda, ei ole minu anda. Minu Isa on see, kes seda otsustab.“
24 Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.
Kui ülejäänud kümme jüngrit kuulsid, mida nad olid palunud, olid nad kahe venna peale pahased.
25 Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, ''Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko.
Jeesus kutsus nad kokku ja rääkis neile: „Te teate, et võõramaised valitsejad valitsevad oma alamate üle ja võimukad juhid rõhuvad neid.
26 Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku.
Teie puhul ei tohi see nii olla. Kes iganes teist soovib olla kõige tähtsam, see olgu teie teenija.
27 Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku.
Kes iganes teist soovib olla tähtsaim, olgu nagu ori.
28 Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa.''
Samamoodi ei tulnud inimese Poeg, et teda teenitaks, vaid ta tuli teenima ja andma oma elu lunarahaks paljude eest.“
29 Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi.
Kui nad Jeerikost lahkusid, järgis Jeesust tohutu rahvahulk.
30 Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
Tee ääres istus kaks pimedat meest. Kui nad kuulsid, et Jeesus on mööda minemas, hüüdsid nad: „Halasta meie peale, Issand, Taaveti poeg!“
31 Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
Rahvas käskis neil vait olla, aga nad hüüdsid veel valjemini: „Halasta meie peale, Issand, Taaveti poeg!“
32 Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, ''Me kuke so in yi maku?''
Jeesus peatus. Ta kutsus nad enda juurde ja küsis: „Mida te tahate, et ma teile teeksin?“
33 Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.''
„Issand, palun tee meid jälle nägijateks, “vastasid nad.
34 Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
Jeesusel oli neist kahju ja ta puudutas nende silmi. Kohe nägid nad jälle ja järgisid teda.