< Mattiyu 2 >

1 Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa,
Da Jesus var født i Betlehem i Judea, i kong Herodes' dager, se, da kom nogen vismenn fra Østerland til Jerusalem og sa:
2 ''Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada.''
Hvor er den jødenes konge som nu er født? Vi har sett hans stjerne i Østen og er kommet for å tilbede ham.
3 Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.
Men da kong Herodes hørte det, blev han forferdet, og hele Jerusalem med ham.
4 Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, “Ina za a haifi Almasihun?”
Og han sammenkalte alle yppersteprestene og de skriftlærde blandt folket og spurte dem hvor Messias skulde fødes.
5 Suka ce masa, ''A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta,
De sa til ham: I Betlehem i Judea; for så er skrevet ved profeten:
6 'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'''
Og du Betlehem i Juda land, du er ingenlunde den ringeste blandt høvdingene i Juda; for fra dig skal utgå en høvding som skal være hyrde for mitt folk Israel.
7 Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana.
Da kalte Herodes hemmelig vismennene til sig og spurte dem nøie om tiden da stjernen hadde vist sig;
8 Ya aike su Baitalami, ya ce, ''Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada.”
og han sendte dem til Betlehem og sa: Gå og spør nøie om barnet; og når I har funnet det, da si mig til, forat også jeg kan komme og tilbede det!
9 Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake.
Da de hadde hørt kongens ord, drog de avsted; og se, stjernen som de hadde sett i Østen, gikk foran dem, inntil den kom og blev stående over det sted hvor barnet var.
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.
Og da de så stjernen, blev de over all måte glade.
11 Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur.
Og de gikk inn i huset og så barnet med Maria, dets mor, og de falt ned og tilbad det, og oplot sine gjemmer og bar frem gaver til det: gull og røkelse og myrra.
12 Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.
Og da de var blitt varslet av Gud i en drøm at de ikke skulde vende tilbake til Herodes, drog de en annen vei bort til sitt land.
13 Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, ''Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi.”
Men da de hadde draget bort, se, da åpenbarer Herrens engel sig i en drøm for Josef og sier: Stå op, ta barnet og dets mor og fly til Egypten, og bli der inntil jeg sier dig til! for Herodes vil søke efter barnet for å drepe det.
14 A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar.
Da stod han op og tok barnet og dets mor om natten og drog bort til Egypten,
15 Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, ''Daga Masar na kirawo Da na.''
og han blev der til Herodes' død, forat det skulde opfylles som er talt av Herren ved profeten, som sier: Fra Egypten kalte jeg min sønn.
16 Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.
Da Herodes nu så at han var blitt narret av vismennene, blev han meget vred, og han sendte bud og lot drepe alle de guttebarn som var i Betlehem og alt landet deromkring, fra to år og derunder, efter den tid han nøie hadde utspurt av vismennene.
17 A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya,
Da blev det opfylt som er talt ved profeten Jeremias, som sier:
18 ''An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.
En røst blev hørt i Rama, gråt og stor klage; Rakel gråt over sine barn og vilde ikke la sig trøste, for de er ikke mere til.
19 Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce,
Men da Herodes var død, se, da åpenbarer Herrens engel sig i en drøm for Josef i Egypten og sier:
20 ''Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu.''
Stå op, ta barnet og dets mor og dra til Israels land! for de er døde som stod barnet efter livet.
21 Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.
Og han stod op og tok barnet og dets mor og kom til Israels land.
22 Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili
Men da han hørte at Arkelaus var konge i Judea efter sin far Herodes, fryktet han for å dra dit; men han blev varslet av Gud i en drøm og drog bort til Galilea.
23 sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.
Og han kom og tok bolig i en by som heter Nasaret, forat det skulde opfylles som er talt ved profetene, at han skal kalles en nasareer.

< Mattiyu 2 >