< Mattiyu 16 >

1 Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama.
Tudi farizeji so prišli skupaj s saduceji in ga skušali ter zahtevali, da bi jim pokazal znamenje z neba.
2 Amma ya amsa ya ce masu, “Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'
Odgovoril je in jim rekel: »Ko je večer, pravite: ›Lepo vreme bo, kajti nebo je rdeče.‹
3 Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba.
Zjutraj pa: ›Danes bo grdo vreme, kajti nebo je rdeče in mračno.‹ O vi hinavci, lahko razpoznavate obličje neba, toda ne morete razpoznati znamenj časov?
4 Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa.” Daga nan sai Yesu ya tafi.
Zlobni in zakonolomni rod išče znamenje, pa mu ne bo dano nobeno znamenje, razen znamenja preroka Jona.« In zapustil jih je ter odšel.
5 Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa,
Ko so njegovi učenci prišli na drugo stran, so pozabili vzeti kruh.
6 Yesu ya ce masu, “Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa.”
Potem jim je Jezus rekel: »Pazite in varujte se kvasa farizejev in saducejev.«
7 Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, “Ko saboda bamu kawo gurasa bane.”
In med seboj so razpravljali, rekoč: » To je zato, ker nismo vzeli kruha.«
8 Yesu yana sane da wannan sai ya ce, “Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
Ko je Jezus to zaznal, jim je rekel: »Oh vi maloverni, zakaj med seboj razmišljate, ker niste prinesli nobenega kruha?
9 Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba?
Ali še vedno ne razumete niti se ne spominjate petih hlebov pet tisočim in koliko košar ste pobrali?
10 Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
Niti sedmih hlebov štiri tisočim in koliko košar ste pobrali?
11 Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa.”
Kako to, da ne razumete, da vam tega nisem govoril v zvezi s kruhom, da bi se varovali kvasa farizejev in saducejev?«
12 Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
Potem so razumeli, da jim je zaukazal, naj se ne varujejo kruhovega kvasa, temveč nauka farizejev in saducejev.
13 A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, “Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake?
Ko je Jezus prišel v kraje Cezareje Filipove, je vprašal svoje učence, rekoč: »Kdo ljudje pravijo, da jaz, Sin človekov, sem?«
14 Suka ce, “Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa.”
Rekli so: »Nekateri pravijo, da si Janez Krstnik, nekateri Elija in drugi Jeremija ali eden izmed prerokov.«
15 Ya ce masu, “Amma ku wa kuke ce da ni?”
Reče jim: »Toda kdo vi pravite, da sem jaz?«
16 Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai.”
In Simon Peter je odgovoril ter rekel: »Ti si Kristus, Sin živega Boga.«
17 Yesu ya amsa ya ce masa, “Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama.
In Jezus je odgovoril ter mu rekel: »Blagoslovljen si, Simon, Jonov sin, kajti meso in kri ti tega nista razodela, temveč moj Oče, ki je v nebesih.
18 Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba. (Hadēs g86)
In jaz ti prav tako pravim: ›Da si ti Peter in na tej skali bom zgradil svojo cerkev in velika vrata pekla ne bodo prevladala proti njej. (Hadēs g86)
19 Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama,”
In dal ti bom ključe nebeškega kraljestva; in karkoli boš zvezal na zemlji, bo zvezano v nebesih; in karkoli boš razvezal na zemlji, bo razvezano v nebesih.‹«
20 Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
Tedaj je svojim učencem naročil, da naj nobenemu človeku ne povedo, da je bil on Jezus, Kristus.
21 Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku.
Od tedaj naprej je Jezus svojim učencem začel kazati, da mora oditi v Jeruzalem in od starešin in visokih duhovnikov in pisarjev pretrpeti mnoge stvari in biti umorjen in tretji dan obujen.
22 Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, “Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba.”
Potem ga je Peter prijel in ga začel oštevati, rekoč: »To naj bo daleč od tebe, Gospod. To naj se ti ne zgodi.«
23 Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane.”
Toda on se je obrnil in Petru rekel: »Spravi se za menoj, Satan. V spotiko si mi, kajti ne posvečaš se stvarem, ki so od Boga, temveč tem, ki so od ljudi.«
24 Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni.
Tedaj je Jezus rekel svojim učencem: »Če hoče katerikoli človek slediti meni, naj se odpove samemu sebi in vzame svoj križ ter hodi za menoj.
25 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi.
Kajti kdorkoli hoče rešiti svoje življenje, ga bo izgubil, kdorkoli pa bo izgubil svoje življenje zaradi mene, ga bo našel.
26 Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
Kajti kaj človeku koristi, če si bo pridobil ves svet, izgubil pa svojo lastno dušo? Ali kaj bo človek dal v zameno za svojo dušo?
27 Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa.
Kajti Sin človekov bo prišel v slavi svojega Očeta s svojimi angeli in tedaj bo vsakega človeka nagradil glede na njegova dela.
28 Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa.”
Resnično, povem vam: ›Tam bo nekaj tukaj navzočih, ki ne bodo okusili smrti, dokler ne vidijo Sina človekovega prihajati v svojem kraljestvu.‹«

< Mattiyu 16 >