< Mattiyu 16 >
1 Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama.
Og Farisæerne og Saddukæerne kom hen og fristede ham og begærede, at han vilde vise dem et Tegn fra Himmelen.
2 Amma ya amsa ya ce masu, “Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'
Men han svarede og sagde til dem: "Om Aftenen sige I: Det bliver en skøn Dag, thi Himmelen er rød;
3 Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba.
og om Morgenen: Det bliver Storm i Dag, thi Himmelen er rød og mørk. Om Himmelens Udseende vide I at dømme, men om Tidernes Tegn kunne I det, ikke.
4 Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa.” Daga nan sai Yesu ya tafi.
En ond og utro Slægt forlanger Tegn; men der skal intet Tegn gives den uden Jonas's Tegn." Og han forlod dem og gik bort.
5 Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa,
Og da hans Disciple kom over til hin Side, havde de glemt at tage Brød med.
6 Yesu ya ce masu, “Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa.”
Og Jesus sagde til dem: "Ser til, og tager eder i Vare for Farisæernes og Saddukæernes Surdejg!"
7 Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, “Ko saboda bamu kawo gurasa bane.”
Men de tænkte ved sig selv og sagde: "Det er, fordi vi ikke toge Brød med."
8 Yesu yana sane da wannan sai ya ce, “Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
Men da Jesus mærkede dette, sagde han: "I lidettroende! hvorfor tænke I ved eder selv på, at I ikke have taget Brød med?
9 Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba?
Forstå I ikke endnu? Komme I heller ikke i Hu de fem Brød til de fem Tusinde, og hvor mange Kurve I da toge op?
10 Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
Ikke heller de syv Brød til de fire Tusinde, og hvor mange Kurve I da toge op?
11 Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa.”
Hvorledes forstå I da ikke, at det ej var om Brød, jeg sagde det til eder? Men tager eder i Vare for Farisæernes og Saddukæernes Surdejg."
12 Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
Da forstode de, at han havde ikke sagt, at de skulde tage sig i Vare for Surdejgen i Brød, men for Farisæernes og Saddukæernes Lære.
13 A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, “Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake?
Men da Jesus var kommen til Egnen ved Kæsarea Filippi, spurgte han sine Disciple og sagde: "Hvem sige Folk, at Menneskesønnen er?"
14 Suka ce, “Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa.”
Men de sagde: "Nogle sige Johannes Døberen; andre Elias; andre Jeremias eller en af Profeterne."
15 Ya ce masu, “Amma ku wa kuke ce da ni?”
Han siger til dem: "Men I, hvem sige I, at jeg er?"
16 Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai.”
Da svarede Simon Peter og sagde: "Du er Kristus, den levende Guds Søn."
17 Yesu ya amsa ya ce masa, “Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama.
Og Jesus svarede og sagde til ham: "Salig er du, Simon Jonas's Søn! thi Kød og Blod har ikke åbenbaret dig det, men min Fader, som er i Himlene.
18 Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba. (Hadēs )
Så siger jeg også dig, at du er Petrus, og på denne Klippe vil jeg bygge min Menighed, og Dødsrigets Porte skulle ikke få Overhånd over den. (Hadēs )
19 Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama,”
Og jeg vil give dig Himmeriges Riges Nøgler, og hvad du binder på Jorden, det skal være bundet i Himlene, og hvad du løser på Jorden, det skal være løst i Himlene."
20 Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
Da bød han sine Disciple, at de måtte ikke sige til nogen at han var Kristus.
21 Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku.
Fra den Tid begyndte Jesus at give sine Disciple til Kende, at han skulde gå til Jerusalem og lide meget af de Ældste og Ypperstepræsterne og de skriftkloge og ihjelslås og oprejses på den tredje Dag.
22 Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, “Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba.”
Og Peter tog ham til Side, begyndte at sætte ham i Rette og sagde: "Gud bevare dig, Herre; dette skal ingenlunde ske dig!"
23 Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane.”
Men han vendte sig og sagde til Peter: "Vig bag mig, Satan! du er mig en Forargelse; thi du sanser ikke, hvad Guds er, men hvad Menneskers er."
24 Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni.
Da sagde Jesus til sine Disciple: "Vil nogen komme efter mig, han fornægte sig selv og tage sit Kors op og følge mig!
25 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi.
Thi den, som vil frelse sit. Liv, skal miste det; men den, som mister sit Liv for min Skyld, skal bjærge det.
26 Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
Thi hvad gavner det et Menneske, om han vinder den hele Verden, men må bøde med sin Sjæl? Eller hvad kan et Menneske give til Vederlag for sin Sjæl?
27 Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa.
Thi Menneskesønnen skal komme i sin Faders Herlighed med sine Engle; og da skal han betale enhver efter hans Gerning.
28 Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa.”
Sandelig siger jeg eder, der er nogle af dem, som stå her, der ingenlunde skulle smage Døden, førend de se Menneskesønnen komme i sit Rige."