< Mattiyu 14 >

1 A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu.
C'est vers ce moment que le tétrarque Hérode entendit parler de Jésus.
2 Ya ce wa barorinsa, “Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa”.
«Cet homme, dit-il, à ses courtisans, c'est Jean-Baptiste! Il est ressuscité d'entre les morts! De là, ces puissances miraculeuses qui agissent en lui!»
3 Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus.
Hérode, en effet, avait arrêté Jean, l'avait garrotté et jeté en prison: et cela à cause d'Hérodiade, la femme de son frère Philippe,
4 Ya ce masa, “Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba.”
et parce que Jean lui disait: «Il ne t'est pas permis d'avoir cette femme-là.»
5 Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
Hérode eût bien voulu le mettre à mort, mais il avait peur du peuple, lequel tenait Jean pour prophète.
6 Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus.
Or, au jour anniversaire de la naissance d'Hérode, la fille d'Hérodiade ayant dansé au milieu de la salle, avait tellement plu au tétrarque
7 Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
qu'il lui avait juré, par serment, de lui accorder tout ce qu'elle lui demanderait.
8 Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, “Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire.
«Donne-moi, lui avait-elle dit alors, poussée par sa mère, ici même, sur un plat, la tête de Jean Baptiste.»
9 Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
Le roi en avait été attristé; cependant à cause de son serment, à cause aussi des convives, il avait commandé de la lui donner
10 Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku.
et d'aller décapiter Jean dans la prison.
11 Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta.
Sa tête avait été apportée sur un plat et donnée à la jeune fille, qui l'avait remise à sa mère.
12 Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
Les disciples de Jean étaient venus prendre son corps et l'ensevelir; puis ils étaient allés en informer Jésus.
13 Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen.
Ayant appris cet événement, Jésus partit de là en barque pour se retirer à l'écart dans quelque endroit solitaire. Mais les troupes, l'ayant su, sortirent des villes et le suivirent à pied,
14 Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
et en débarquant il vit une foule immense, il en eut compassion et il guérit leurs malades.
15 Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, “Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci.”
Sur le soir, les disciples s'approchèrent de lui et lui dirent: «L'endroit est désert et l'heure est déjà avancée, renvoie donc les foules, afin que les uns et les autres aillent dans les villages acheter de quoi se nourrir.)
16 Amma Yesu ya ce masu, “Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci.”
Mais Jésus leur dit: «Il n'est pas nécessaire qu'ils s'en aillent; donnez-leur vous-mêmes à manger.»
17 Suka ce masa, “Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai.”
«Mais, répondirent-ils, nous n'avons ici que cinq pains et deux poissons.»
18 Yesu ya ce, “Ku kawo mani su.”
Il dit: «Apportez-les-moi ici»,
19 Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron.
et, après avoir commandé que la multitude s'assît sur l'herbe, il prit les cinq pains et les deux poissons, et, levant les yeux au ciel, il prononça la bénédiction, puis il rompit les pains, les donna aux disciples et les disciples aux foules.
20 Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike.
Tous mangèrent, tous furent rassasiés, et on emporta les morceaux qui restaient: douze paniers pleins.
21 Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
Quant au nombre de ceux qui avaient mangé, il était de cinq mille hommes environ, sans compter des femmes et des enfants.
22 Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron.
Aussitôt après, il pressa les disciples de remonter dans la barque et de le précéder sur la rive opposée, tandis qu'il renverrait les multitudes.
23 Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai.
Quand il les eut renvoyées, il gravit la montagne afin de prier dans la solitude. Le soir vint et il était seul en ce lieu.
24 Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
Pendant ce temps la barque, déjà au milieu de la mer, était battue des flots, ayant le vent contraire.
25 Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku.
Or, à la quatrième veille de la nuit, il vint à eux en marchant sur la mer.
26 Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, “Fatalwa ce,” suka yi kururuwa cikin tsoro.
Quand les disciples le virent, marchant sur la mer, ils furent bouleversés. «C'est un fantôme», dirent-ils, en jetant des cris de terreur.
27 Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, “Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro.”
Mais aussitôt il leur parla, il leur dit: «Rassurez-vous; c'est moi, soyez sans crainte.»
28 Bitrus ya amsa masa cewa, “Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan.”
Pierre alors s'adressa à lui: Si c'est toi, Seigneur, commande que je vienne à toi sur les flots.» —
29 Yesu yace, “Zo” Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu.
«Viens», dit Jésus. Descendant de la barque, Pierre marcha sur les flots et alla vers Jésus;
30 Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
mais quand il sentit le vent il fut pris de peur et commença à s'enfoncer, alors il s'écria: «Seigneur, sauve-moi.»
31 Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, “Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?”
Jésus étendit immédiatement la main et lui dit en le saisissant: «Homme de peu de foi, pourquoi as-tu douté?»
32 Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa.
Ils entrèrent dans la barque et le vent cessa.
33 Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, “Hakika kai Dan Allah ne.”
Alors ceux qui s'y trouvaient se prosternèrent devant lui, disant: «Tu es vraiment Fils de Dieu.»
34 Da suka haye, sun iso kasar Janisarata.
Ayant passé l'eau, ils arrivèrent au pays de Gennesaret.
35 Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya.
Les gens de l'endroit, l'ayant reconnu, firent prévenir tout le voisinage et lui présentèrent tous leurs malades,
36 Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.
le priant de les laisser seulement toucher la frange de son vêtement. Et tous ceux qui la touchèrent furent guéris.

< Mattiyu 14 >