< Mattiyu 14 >
1 A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu.
During that time Herod [Antipas], the ruler, heard reports about Jesus [performing miracles].
2 Ya ce wa barorinsa, “Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa”.
He said to his servants: “That must be John the Baptizer. He must have risen from the dead, and that is why he has power to perform miracles.”
3 Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus.
The reason [Herod thought that was this: Herod had married] Herodias, the wife of his brother Philip, [while Philip was still living. So] John had been saying to him, “[What] you [did by] marrying [your brother’s wife while your brother is still alive is against God’s] law!” Then, to [please] Herodias, Herod [told his soldiers] to arrest John. They bound him with chains and put him in prison.
4 Ya ce masa, “Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba.”
5 Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
Herod wanted to have John executed, but he was afraid that the people [who had accepted what John taught would riot if he did that], because they believed that John was a prophet.
6 Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus.
But when Herod [gave a party to celebrate] his birthday, the daughter of Herodias danced for [his guests]. This pleased Herod.
7 Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
So he promised to give her whatever she asked, and he asked God to punish him if he did not do what he had promised.
8 Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, “Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire.
[So Herodias’ daughter went and asked her mother what to ask for]. Her mother told her to ask for John the Baptizer’s head. [So] her daughter [went back and] said [to Herod]: “[Cut off] the head of John the Baptizer and [please] bring it here on a platter [so that my mother can know for sure that he is dead!]”
9 Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
The king was distressed because he now knew he should not have made that promise to her. [But] because he had made an oath [in front of] his guests [when he made that promise], and [he did not want] them [to think that he would not do what he had promised], he commanded that [the girl] be given [what she requested].
10 Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku.
He sent [the executioner to go to] the prison and to cut off John’s head.
11 Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta.
[The executioner did that, and] put John’s head on a platter and gave it to the girl. Then the girl took it to her mother.
12 Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
John’s disciples then went [to the prison], took John’s body and buried it, and they reported to Jesus [what had happened].
13 Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen.
After Jesus heard that, he took [just us disciples] with him and we went by boat [on Galilee Lake to an uninhabited place]. Matthew 14:13-21 After the crowds heard [that we had gone to an uninhabited place], they [left their towns and] followed Jesus, walking along the shore.
14 Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
When Jesus came [to the shore], he saw a large crowd of people [who had gathered there, waiting for him]. He felt sorry for them, and he healed those [among them who were] sick.
15 Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, “Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci.”
When it was [nearly] evening, we disciples came to him and said, “This is a place where nobody lives, and it is very late. Dismiss the crowds so that they can go into the [nearby] towns. [Have them do that so that they can] buy food for themselves.”
16 Amma Yesu ya ce masu, “Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci.”
But Jesus said to us, “They do not need to leave [to get food. Instead], you [yourselves] give them something to eat!”
17 Suka ce masa, “Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai.”
We said to him, “But we have only five loaves of bread and two [cooked] fish here!”
18 Yesu ya ce, “Ku kawo mani su.”
He said [to us], “Bring them to me!”
19 Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron.
He told the people [who had gathered there] to sit on the grass. Then he took the five flat loaves and the two fish. He looked up toward heaven, thanked [God for them], and broke [them into pieces]. Then he gave them to us disciples, and we distributed them to the crowd.
20 Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike.
All [the people in the crowd] ate until they had enough to eat. Then we [disciples] gathered the pieces that were left over, [and we] filled twelve baskets with them.
21 Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
Those who ate were about 5,000 men. [We did] not [count the] women and children!
22 Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron.
Right after that happened, Jesus told us disciples to get in the boat and to go ahead of him further around [the lake] while he dismissed the crowds.
23 Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai.
After he dismissed them, he went up into the hills to pray by himself. When it was evening, he was [still] there alone.
24 Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
[By this time] we were already many hundred meters from the shore. The boat was being severely tossed around by the waves {The waves were severely tossing the boat} because the wind was [blowing] against [it].
25 Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku.
[Then Jesus came down from the hills to the lake]. Some time between three and six o’clock in the morning he walked on the water toward our [boat].
26 Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, “Fatalwa ce,” suka yi kururuwa cikin tsoro.
When we disciples saw someone walking on the water, we thought that [we must be seeing] a ghost. We were terrified, and we screamed out because we were afraid.
27 Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, “Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro.”
Immediately Jesus said to us, “Cheer up! It is I. Do not be afraid!”
28 Bitrus ya amsa masa cewa, “Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan.”
Peter said to him, “Lord, if it is you, tell me to walk on the water to you!”
29 Yesu yace, “Zo” Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu.
Then Jesus said, “Come!” So Peter got out of the boat and walked on the water toward Jesus.
30 Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
But when Peter looked at the [tossing waves which] the strong wind [caused], he became afraid. He began to sink, and cried out, “Lord, save me!”
31 Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, “Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?”
Immediately Jesus stretched out his hand and grabbed him. He said to Peter, “You only trust a little bit [in my power] (Why did you doubt [that I could keep you from sinking]?/You should not have doubted [that I could keep you from sinking]!) [RHQ]”
32 Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa.
Then Jesus and Peter got in the boat, and the wind [immediately] stopped blowing.
33 Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, “Hakika kai Dan Allah ne.”
All [of us disciples] who were in the boat worshipped Jesus and said, “Truly you are the (Son of/man two is also) God!”
34 Da suka haye, sun iso kasar Janisarata.
When we had gone further around [the lake in the boat], we came ashore at Gennesaret [town].
35 Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya.
The men of that area recognized Jesus. So they sent [people to inform those who lived] in that whole surrounding region [MTY] [that Jesus was in their area]. [So the people] brought to Jesus all the sick people [who lived in that region].
36 Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.
[The sick people] kept begging him to allow them to touch [him or] just to touch the edge of his robe [so that they would be healed]. And all who touched [him or his robe] were healed {he healed all who touched [him or his clothing]}.