< Mattiyu 12 >
1 A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
Ob tistem času je šel Jezus na šabatni dan skozi žitna polja, njegovi učenci pa so bili lačni in začeli smukati žitno klasje ter jesti.
2 Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
Toda ko so to videli farizeji, so mu rekli: »Glej, tvoji učenci delajo to, česar ni zakonito početi na šabatni dan.«
3 Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
Toda rekel jim je: »Ali niste brali, kaj je storil David, ko je bil lačen in tisti, ki so bili z njim,
4 Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
kako je vstopil v Božjo hišo in jedel hlebe navzočnosti, ki jih ni bilo dovoljeno jesti njemu niti ne tistim, ki so bili z njim, temveč samo duhovnikom?
5 Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
Ali niste brali v postavi, kako to, da ob šabatnih dneh duhovniki v templju skrunijo šabat in so brez krivde?
6 Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
Toda povem vam: ›Da je na tem kraju nekdo večji kakor tempelj.‹
7 In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
Toda če bi vedeli, kaj to pomeni: ›Usmiljenje hočem imeti in ne žrtve, ‹ ne bi obsojali nedolžnih.
8 Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
Kajti Sin človekov je Gospod celó šabatnemu dnevu.«
9 Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
In ko je odšel od tam, je šel v njihovo sinagogo.
10 Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
In glej, tam je bil človek, ki je imel svojo roko izsušeno. In da bi ga lahko obdolžili, so ga vprašali, rekoč: »Ali je zakonito zdraviti na šabatne dneve?«
11 Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
In rekel jim je: »Kateri človek bi bil tukaj med vami, ki bi imel eno ovco in če bi ta na šabatni dan padla v jamo ali je ne bi prijel ter je dvignil ven?
12 Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
Koliko bolj je potem človek boljši kakor ovca? Zaradi tega je na šabatne dneve zakonito delati dobro.«
13 Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
Tedaj reče človeku: »Iztegni svojo roko.« In ta jo je iztegnil in bila je v celoti ozdravljena, podobno kakor druga.
14 Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
Potem so farizeji odšli ven in imeli zborovanje proti njemu, kako bi ga lahko pokončali.
15 Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
Toda ko je Jezus to izvedel, se je umaknil od tam in sledile so mu velike množice in vse je ozdravil
16 Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
ter jim naročil, da naj ga ne razglašajo,
17 domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
da bi se lahko izpolnilo, kar je bilo rečeno po preroku Izaiju, rekoč:
18 “Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
›Glej moj služabnik, ki sem ga izbral, moj ljubljeni, v katerem je moja duša zelo zadovoljna. Svojega duha bom položil nadenj in oznanil bo sodbo poganom.
19 Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
Ne bo se ne prepiral niti ne vpil niti na ulicah nihče ne bo slišal njegovega glasu.
20 Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
Poškodovanega trsta ne bo zlomil in kadečega stenja ne bo pogasil, dokler ne privede sodbe do zmage.
21 Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
In v njegovo ime bodo zaupali pogani.‹
22 Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
Tedaj je bil k njemu priveden nekdo obseden s hudičem, slep in nem in ga je ozdravil, do take mere, da je slepi in nemi tako govoril kakor videl.
23 Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
In vsa množica je bila osupla ter rekla: »Ali ni ta Davidov sin?«
24 Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
Toda ko so farizeji to slišali, so rekli: »Ta ne izganja hudičev, razen z Bélcebubom, princem hudičev.«
25 Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
Jezus pa je poznal njihove misli in jim rekel: »Vsako kraljestvo, razdeljeno zoper sebe, je privedeno v opustošenje in nobeno mesto ali hiša, razdeljena zoper sebe, ne bosta obstala.
26 Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
In če Satan izganja Satana, je razdeljen zoper sebe; kako bo potem obstalo njegovo kraljestvo?
27 Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
In če z Bélcebubom izganjam hudiče, s kom jih izganjajo vaši otroci? Zatorej bodo oni vaši sodniki.
28 Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
Toda če z Božjim Duhom izganjam hudiče, potem je k vam prišlo Božje kraljestvo.
29 Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
Kako lahko sicer nekdo vstopi v hišo močnega in opleni njegove dobrine, razen če najprej ne zveže močnega? In tedaj bo oplenil njegovo hišo.
30 Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
Kdor ni z menoj, je proti meni; in kdor ne zbira z menoj, razsipa na široko.
31 Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
Zatorej vam pravim: ›Vsake vrste greh in bogokletje bo ljudem odpuščeno, toda bogokletje zoper Svetega Duha ljudem ne bo odpuščeno.
32 Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn )
In kdorkoli govori besedo zoper Sina človekovega, mu bo to odpuščeno; toda kdorkoli govori zoper Svetega Duha, mu ne bo odpuščeno ne na tem svetu ne v svetu, ki pride.‹ (aiōn )
33 Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
Ali drevo dobro obrodi in je njegov sad dober, ali pa drevo slabo obrodi in je njegov sad slab; kajti drevo se spozna po njegovem sadu.
34 Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
Oh gadji rod, kako lahko vi, ki ste hudobni, govorite dobre besede? Kajti iz obilja srca usta govoré.
35 Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
Dober človek iz dobrega zaklada srca prinaša dobre stvari, hudobnež pa iz zlega zaklada prinaša zle stvari.
36 Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
Toda povem vam: ›Za vsako prazno besedo, ki jo bodo ljudje izgovorili, bodo na dan sodbe o tem dajali obračun.‹
37 Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
Kajti po svojih besedah boš opravičen in po svojih besedah boš obsojen.«
38 Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
Tedaj so nekateri izmed pisarjev in farizejev odgovorili, rekoč: »Učitelj, od tebe želimo videti znamenje.«
39 Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
Toda odgovoril jim je in rekel: »Hudoben in zakonolomen rod išče znamenje, pa mu ne bo dano nobeno drugo znamenje, razen znamenja preroka Jona.
40 Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
Kajti tako, kakor je bil Jona tri dni in tri noči v kitovem trebuhu, tako bo Sin človekov tri dni in tri noči v osrčju zemlje.
41 Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
Ljudje iz Niniv bodo ob sodbi vstali s tem rodom in ga obsodili, ker so se ob Jonovem oznanjevanju pokesali; in glejte, tukaj je večji kakor Jona.
42 Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
Kraljica z juga bo ob sodbi vstala s tem rodom in ga obsodila, kajti prišla je iz najbolj oddaljenih krajev zemlje, da sliši Salomonovo modrost; in glejte, tukaj je večji kakor Salomon.
43 Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
Kadar je nečisti duh odšel iz človeka, hodi po suhih krajih, iščoč počitka, in ga ne najde.
44 Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
Potem reče: ›Vrnil se bom v svojo hišo, od koder sem izšel.‹ In ko pride, jo najde prazno, pometeno in okrašeno.
45 Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
Tedaj gre in s seboj vzame sedem drugih duhov, zlobnejših kakor on sam in vstopijo ter prebivajo tam in končno stanje tega človeka je slabše kakor prvo. Točno tako bo tudi temu zlobnemu rodu.«
46 Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
Medtem ko je še govoril množici, glej, so stali zunaj njegova mati in njegovi bratje, želeč govoriti z njim.
47 Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
Potem mu je nekdo rekel: »Glej, tvoja mati in tvoji bratje stojijo zunaj in želijo govoriti s teboj.«
48 Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
Toda odgovoril je in rekel tistemu, ki mu je povedal: »Kdo je moja mati? In kdo so moji bratje?«
49 Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
In svojo roko je iztegnil proti svojim učencem ter rekel: »Glejte, moja mati in moji bratje!
50 Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”
Kajti kdorkoli bo izvrševal voljo mojega Očeta, ki je v nebesih, ta je moj brat in sestra in mati.«