< Mattiyu 12 >

1 A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
På den Tid vandrede Jesus på Sabbaten igennem en Sædemark; men hans Disciple bleve hungrige og begyndte at plukke Aks og at spise.
2 Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
Men da Farisæerne så det, sagde de til ham: "Se, dine Disciple gøre, hvad det ikke er tilladt at gøre på en Sabbat."
3 Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
Men han sagde til dem: "Have I ikke læst, hvad David gjorde, da han blev hungrig og de, som vare med ham?
4 Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
hvorledes han gik ind i Guds Hus og spiste Skuebrødene, som det ikke var ham tilladt at spise, ej heller dem, som vare med ham, men alene Præsterne?
5 Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
Eller have I ikke læst i Loven, at på Sabbaterne vanhellige Præsterne Sabbaten i Helligdommen og ere dog uden Skyld?
6 Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
Men jeg siger eder, at her er det, som er større end Helligdommen.
7 In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
Men dersom I havde vidst, hvad det Ord betyder: Jeg har Lyst til Barmhjertighed og ikke til Offer, da havde I ikke fordømt dem, som ere uden Skyld.
8 Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
Thi Menneskesønnen er Herre over Sabbaten."
9 Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
Og han gik videre derfra og kom ind i deres Synagoge.
10 Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
Og se, der var en Mand, som havde en vissen Hånd; og de spurgte ham ad og sagde: "Er det tilladt at helbrede på Sabbaten?" for at de kunde anklage ham.
11 Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
Men han sagde til dem: "Hvilket Menneske er der iblandt eder, som har kun eet Får, og ikke tager fat på det og drager det op, dersom det på Sabbaten falder i en Grav?
12 Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
Hvor meget er nu ikke et Menneske mere end et Får? Altså er det tilladt at gøre vel på Sabbaten."
13 Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
Da siger han til Manden: "Ræk din Hånd ud!" og han rakte den ud, og den blev igen sund som den anden.
14 Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
Men Farisæerne gik ud og lagde Råd op imod ham, hvorledes de kunde slå ham ihjel.
15 Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
Men da Jesus mærkede det, drog han bort derfra; og mange fulgte ham, og han helbredte dem alle.
16 Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
Og han bød dem strengt, at de ikke måtte gøre ham kendt;
17 domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
for at det skulde opfyldes, som er talt ved Profeten Esajas, som siger:
18 “Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
"Se, min Tjener, som jeg har udvalgt, min elskede, i hvem min Sjæl har Velbehag; jeg vil give min Ånd over ham, og han skal forkynde Hedningerne Ret.
19 Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
Han skal ikke kives og ikke råbe, og ingen skal høre hans Røst på Gaderne.
20 Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
Han skal ikke sønderbryde det knækkede Rør og ikke udslukke den rygende Tande, indtil han får ført Retten frem til Sejr.
21 Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
Og på hans Navn skulle Hedninger håbe."
22 Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
Da blev en besat, som var blind og stum, ført til ham; og han helbredte ham, så at den stumme talte og så.
23 Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
Og alle Skarerne forfærdedes og sagde: "Mon denne skulde være Davids Søn?"
24 Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
Men da Farisæerne hørte det, sagde de: "Denne uddriver ikke de onde Ånder uden ved Beelzebul, de onde Ånders Fyrste."
25 Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
Men såsom han kendte deres Tanker, sagde han til dem: "Hvert Rige, som er kommet i Splid med sig selv, lægges øde; og hver By eller Hus, som er kommet i Splid med sig selv, kan ikke bestå.
26 Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
Og hvis Satan uddriver Satan, så er han kommen i Splid med sig selv; hvorledes skal da hans Rige bestå?
27 Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
Og dersom jeg uddriver de onde Ånder ved Beelzebul, ved hvem uddrive da eders Sønner dem? Derfor skulle de være eders Dommere.
28 Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
Men dersom jeg uddriver de onde Ånder ved Guds Ånd, da er jo Guds Rige kommet til eder.
29 Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
Eller hvorledes kan nogen gå ind i den stærkes Hus og røve hans Ejendele, uden han først binder den stærke? Da kan han plyndre hans Hus.
30 Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
Den, som ikke er med mig, er imod mig; og den, som ikke samler med mig, adspreder.
31 Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
Derfor siger jeg eder: Al Synd og Bespottelse skal forlades Menneskene, men Bespottelsen imod Ånden skal ikke forlades.
32 Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn g165)
Og den, som taler et Ord imod Menneskesønnen, ham skal det forlades; men den som taler imod den Helligånd, ham skal det ikke forlades, hverken i denne Verden eller i den kommende. (aiōn g165)
33 Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
Lader enten Træet være godt og dets Frugt god; eller lader Træet være råddent, og dets Frugt rådden; thi Træet kendes på Frugten.
34 Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
I Øgleunger! hvorledes kunne I tale godt, når I ere onde? Thi af Hjertets Overflødighed taler Munden.
35 Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
Et godt Menneske fremtager gode Ting af sit gode Forråd; og et ondt Menneske fremtager onde Ting af sit onde Forråd.
36 Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
Men jeg siger eder, at Menneskene skulle gøre Regnskab på Dommens Dag for hvert utilbørligt Ord, som de tale.
37 Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
Thi af dine Ord skal du retfærdiggøres, og af dine Ord skal du førdømmes."
38 Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
Da svarede nogle af de skriftkloge og Farisæerne ham og sagde: "Mester! vi ønske at se et Tegn at dig."
39 Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
Men han svarede og sagde til dem: "En ond og utro Slægt forlanger Tegn, men der skal intet Tegn gives den uden Profeten Jonas's Tegn.
40 Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
Thi ligesom Jonas var tre Dage og tre Nætter i Havdyrets Bug, således skal Menneskesønnen være tre Dage og tre Nætter i Jordens Skød.
41 Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
Mænd fra Ninive skulle opstå ved Dommen sammen med denne Slægt og fordømme den; thi de omvendte sig ved Jonas's Prædiken; og se, her er mere end Jonas.
42 Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
Sydens Dronning skal oprejses ved Dommen sammen med denne Slægt og fordømme den; thi hun kom fra Jordens Grænser for at høre Salomons Visdom; og se, her er mere end Salomon.
43 Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
Men når den urene Ånd er faren ud af Mennesket, vandrer den igennem vandløse Steder, søger Hvile og finder den ikke.
44 Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
Da siger den: Jeg vil vende om til mit Hus, som jeg gik ud af; og når den kommer, finder den det ledigt, fejet og prydet.
45 Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
Så går den hen og tager syv andre Ånder med sig, som ere værre end den selv, og når de ere komne derind, bo de der; og det sidste bliver værre med dette Menneske end det første. Således skal det også gå denne onde Slægt."
46 Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
Medens han endnu talte til Skarerne, se, da stode hans Moder og hans Brødre udenfor og begærede at tale med ham.
47 Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
Da sagde en til ham: "Se, din Moder og dine Brødre stå udenfor og begære at tale med dig."
48 Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
Men han svarede og sagde til den, som sagde ham det: "Hvem er min Moder? og hvem ere mine Brødre?"
49 Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
Og han rakte sin Hånd ud over sine Disciple og sagde: "Se, her er min Moder og mine Brødre!
50 Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”
Thi enhver, der gør min Faders Villie, som er i Himlene, han er min Broder og Søster og Moder."

< Mattiyu 12 >