< Mattiyu 11 >
1 Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi.
Og det skete, da Jesus var færdig med at give sine tolv Disciple Befaling, gik han videre derfra for at lære og prædike i deres Byer.
2 Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa.
Men da Johannes hørte i Fængselet om Kristi Gerninger, sendte han Bud med sine Disciple og lod ham sige:
3 Ya ce masa. “Kai ne mai zuwa”? ko mu sa ido ga wani.
“Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?”
4 Yesu ya amsa ya ce masu, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji.
Og Jesus svarede og sagde til dem: “Gaar hen, og forkynder Johannes de Ting, som I høre og se:
5 Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara.
blinde se, og lamme gaa, spedalske renses, og døve høre, og døde staa op, og Evangeliet forkyndes for fattige;
6 Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
og salig er den, som ikke forarges paa mig.”
7 Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, “Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa?
Men da disse gik bort, begyndte Jesus at sige til Skarerne om Johannes: “Hvad gik I ud i Ørkenen at skue? Et Rør, som bevæges hid og did af Vinden?
8 Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
Eller hvad gik I ud at se? Et Menneske, iført bløde Klæder? Se, de, som bære bløde Klæder, ere i Kongernes Huse.
9 Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi.
Eller hvad gik I ud at se? En Profet? Ja, siger jeg eder, endog mere end en Profet.
10 Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
Thi han er den, om hvem der er skrevet: Se, jeg sender min Engel for dit Ansigt, han skal berede din Vej foran dig.
11 Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma.
Sandelig, siger jeg eder, iblandt dem, som ere fødte af Kvinder, er ingen større fremstaaet end Johannes Døberen; men den mindste i Himmeriges Rige er større end han.
12 Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
Men fra Johannes Døberens Dage indtil nu tages Himmeriges Rige med Vold, og Voldsmænd rive det til sig.
13 Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya.
Thi alle Profeterne og Loven have profeteret indtil Johannes.
14 kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo.
Og dersom I ville tage imod det: Han er Elias, som skal komme.
15 Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
Den, som har Øren at høre med, han høre!
16 Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna
Men hvem skal jeg ligne denne Slægt ved? Den ligner Børn, som sidde paa Torvene og raabe til de andre og sige:
17 suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
Vi blæste paa Fløjte for eder, og I dansede ikke; vi sang Klagesange, og I jamrede ikke.
18 Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, “Yana da aljannu”.
Thi Johannes kom, som hverken spiste eller drak, og de sige: Han er besat.
19 Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
Menneskesønnen kom, som spiser og drikker, og de sige: Se, en Fraadser og en Vindranker, Tolderes og Synderes Ven! Dog, Visdommen er retfærdiggjort ved sine Børn.”
20 Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba.
Da begyndte han at skamme de Byer ud, i hvilke hans fleste kraftige Gerninger vare gjorte, fordi de ikke havde omvendt sig:
21 “Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka.
“Ve dig, Korazin! ve dig, Bethsajda! thi dersom de kraftige Gerninger, som ere skete i eder, vare skete i Tyrus og Sidon, da havde de for længe siden omvendt sig i Sæk og Aske.
22 Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
Men jeg siger eder: Det skal gaa Tyrus og Sidon taaleligere paa Dommens Dag end eder.
23 Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. (Hadēs )
Og du, Kapernaum! som er bleven ophøjet indtil Himmelen, du skal nedstødes indtil Dødsriget; thi dersom de kraftige Gerninger, som ere skete i dig, vare skete i Sodoma, da var den bleven staaende indtil denne Dag. (Hadēs )
24 Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku.”
Men jeg siger eder: Det skal gaa Sodomas Land taaleligere paa Dommens Dag end dig.”
25 A wannan lokaci Yesu ya ce, “Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara.
Paa den Tid udbrød Jesus og sagde: “Jeg priser dig, Fader, Himmelens og Jordens Herre! fordi du har skjult dette for vise og forstandige og aabenbaret det for umyndige.
26 I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka.
Ja, Fader! thi saaledes skete det, som var velbehageligt for dig.
27 An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
Alle Ting ere mig overgivne af min Fader; og ingen kender Sønnen uden Faderen, og ingen kender Faderen uden Sønnen, og den, for hvem Sønnen vil aabenbare ham.
28 Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa.
Kommer hid til mig alle, som lide Møje og ere besværede, og jeg vil give eder Hvile.
29 Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku.
Tager mit Aag paa eder, og lærer af mig; thi jeg er sagtmodig og ydmyg af Hjertet; saa skulle I finde Hvile for eders Sjæle.
30 Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi.”
Thi mit Aag er gavnligt, og min Byrde er let.”