< Markus 1 >
1 Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
THE beginning of the gospel of Jesus Christ, the Son of God;
2 kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
As it is written in the prophets, Behold, I send my messenger before thy face, which shall prepare thy way before thee.
3 Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
The voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, make his paths straight.
4 Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
John did baptize in the wilderness, and preach the baptism of repentance for the remission of sins.
5 Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
And there went out unto him all the land of Judæa, and they of Jerusalem, and were all baptized of him in the river of Jordan, confessing their sins.
6 Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
And John was clothed with camel’s hair, and with a girdle of a skin about his loins; and he did eat locusts and wild honey;
7 Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
And preached, saying, There cometh one mightier than I after me, the latchet of whose shoes I am not worthy to stoop down and unloose.
8 Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
I indeed have baptized you with water: but he shall baptize you with the Holy Ghost.
9 Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
And it came to pass in those days, that Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized of John in Jordan.
10 Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
And straightway coming up out of the water, he saw the heavens opened, and the Spirit like a dove descending upon him:
11 Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
And there came a voice from heaven, saying, Thou art my beloved Son, in whom I am well pleased.
12 Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
And immediately the Spirit driveth him into the wilderness.
13 Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
And he was there in the wilderness forty days, tempted of Satan; and was with the wild beasts; and the angels ministered unto him.
14 Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
Now after that John was put in prison, Jesus came into Galilee, preaching the gospel of the kingdom of God,
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
And saying, The time is fulfilled, and the kingdom of God is at hand: repent ye, and believe the gospel.
16 Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
Now as he walked by the sea of Galilee, he saw Simon and Andrew his brother casting a net into the sea: for they were fishers.
17 Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
And Jesus said unto them, Come ye after me, and I will make you to become fishers of men.
18 Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
And straightway they forsook their nets, and followed him.
19 Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
And when he had gone a little further thence, he saw James the son of Zebedee, and John his brother, who also were in the ship mending their nets.
20 Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
And straightway he called them: and they left their father Zebedee in the ship with the hired servants, and went after him.
21 Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
And they went into Capernaum; and straightway on the sabbath day he entered into the synagogue, and taught.
22 Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
And they were astonished at his doctrine: for he taught them as one that had authority, and not as the scribes.
23 A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
And there was in their synagogue a man with an unclean spirit; and he cried out,
24 Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
Saying, Let us alone; what have we to do with thee, thou Jesus of Nazareth? art thou come to destroy us? I know thee who thou art, the Holy One of God.
25 Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
And Jesus rebuked him, saying, Hold thy peace, and come out of him.
26 Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
And when the unclean spirit had torn him, and cried with a loud voice, he came out of him.
27 Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
And they were all amazed, insomuch that they questioned among themselves, saying, What thing is this? what new doctrine is this? for with authority commandeth he even the unclean spirits, and they do obey him.
28 Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
And immediately his fame spread abroad throughout all the region round about Galilee.
29 Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
And forthwith, when they were come out of the synagogue, they entered into the house of Simon and Andrew, with James and John.
30 Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
But Simon’s wife’s mother lay sick of a fever, and anon they tell him of her.
31 Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
And he came and took her by the hand, and lifted her up; and immediately the fever left her, and she ministered unto them.
32 Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
And at even, when the sun did set, they brought unto him all that were diseased, and them that were possessed with devils.
33 Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
And all the city was gathered together at the door.
34 ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
And he healed many that were sick of divers diseases, and cast out many devils; and suffered not the devils to speak, because they knew him.
35 Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
And in the morning, rising up a great while before day, he went out, and departed into a solitary place, and there prayed.
36 Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
And Simon and they that were with him followed after him.
37 Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
And when they had found him, they said unto him, All men seek for thee.
38 Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
And he said unto them, Let us go into the next towns, that I may preach there also: for therefore came I forth.
39 Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
And he preached in their synagogues throughout all Galilee, and cast out devils.
40 Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
And there came a leper to him, beseeching him, and kneeling down to him, and saying unto him, If thou wilt, thou canst make me clean.
41 Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
And Jesus, moved with compassion, put forth his hand, and touched him, and saith unto him, I will; be thou clean.
42 Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
And as soon as he had spoken, immediately the leprosy departed from him, and he was cleansed.
43 Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
And he straitly charged him, and forthwith sent him away;
44 Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
And saith unto him, See thou say nothing to any man: but go thy way, shew thyself to the priest, and offer for thy cleansing those things which Moses commanded, for a testimony unto them.
45 Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
But he went out, and began to publish it much, and to blaze abroad the matter, insomuch that Jesus could no more openly enter into the city, but was without in desert places: and they came to him from every quarter.