< Markus 9 >
1 Sai ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, akwai wasun ku anan da ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
And he said to them, Verily I say to you, that there are some of them that stand here who shall not taste death, till they have seen the kingdom of God come with power.
2 Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kadai. Sai kamaninsa ya sake a gabansu.
And after six days, Jesus taketh [with him] Peter, and James, and John, and leadeth them up upon a high mountain apart by themselves; and he was transfigured before them.
3 Sai tufafinsa ya zama fari fat, yadda ba mai rinin da zai iya rininsa haka a duniya.
And his raiment became shining, exceeding white as snow; so as no fuller on earth can whiten them.
4 Sai Iliya da Musa suka bayyana gare su, suna magana da Yesu.
And there appeared to them Elijah, with Moses: and they were talking with Jesus.
5 Sai Bitrus ya amsa ya ce, malam, bari mu da muke anan mu kafa bukka uku, daya ta ka, daya ta Musa, da ta Iliya,
And Peter answered and said to Jesus, Master, it is good for us to be here: and let us make three tabernacles; one for thee, and one for Moses, and one for Elijah.
6 Ya rasa abin da zai fada ne, don sun tsorota kwarai.)
For he knew not what to say: for they were greatly terrified.
7 Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga gajimaren, “ta ce Wannan shine kaunataccen Dana, Ku saurare shi.
And there was a cloud that overshadowed them: and a voice came out of the cloud, saying, This is my beloved Son: hear him.
8 Nan take da suka duba, ba su ga kowa ba, sai Yesu shi kadai.
And suddenly, when they had looked around, they saw no man any more, save Jesus only with themselves.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwabe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan da Dan Mutum ya tashi daga mattatu.
And as they came down from the mountain, he charged them that they should tell no man what things they had seen, till the Son of man were risen from the dead.
10 Sai suka bar zancen a tsakaninsu, amma suka tamabayi junansu “mene ne tashin matattu” ke nufi.
And they kept that saying with themselves, questioning one with another what the rising from the dead should mean.
11 Suka tambaye shi yaya malaman attaura suka ce Iliya zai fara zuwa?”
And they asked him, saying, Why say the scribes that Elijah must first come?
12 Ya ce masu, laile ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwan. Don me a ka rubuta cewa Dan Mutum, zai sha wuya iri iri a kuma ki shi?
And he answered and told them, Elijah verily cometh first, and restoreth all things; and how it is written concerning the Son of man, that he must suffer many things, and be set at naught.
13 Amma ina gaya muku Iliya ya riga, ya zo, amma sun yi masa abin da suke so su yi kamar yadda littatafai suka yi magana a kansa.”
But I say to you, that Elijah is indeed come, and they have done to him whatever they pleased, as it is written concerning him.
14 Sa'adda suka dawo wurin sauran almajiran, suka ga taron jama'a masu yawa suna ta muhawara tare da manyan malaman attaura.
And when he came to [his] disciples, he saw a great multitude about them, and the scribes questioning with them.
15 Da ganin sa, sai dukan taron yayi mamaki kwarai da gaske, suka dungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi.
And immediately all the people, when they beheld him, were greatly amazed, and running to [him], saluted him.
16 Ya tambayi almajiransa, “Wacce muhawara ce kuke yi da su?”
And he asked the scribes, What question ye with them?
17 Daya daga cikin taron ya amsa masa”malam, ga shi na kawo maka dana don yana da beben aljani.
And one of the multitude answered and said, Master, I have brought to thee my son, who hath a dumb spirit;
18 Duk lokacin da ya tasar masa yakan buga shi har kasa, na kuma yi wa almajiranka magana su fitar sun kasa.
And wherever he taketh him, he teareth him; and he foameth and gnasheth with his teeth, and pineth away; and I spoke to thy disciples that they should cast him out, and they could not.
19 Ya amsa masu ya ce ya ku mutanen zamaninnan marasa bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku ina jimrewa? ku dai kawo mini shi.
He answered him, and saith, O faithless generation, how long shall I be with you, how long shall I suffer you? bring him to me.
20 Sai suka kawo masa yaron. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan ya buge yaron jikinsa na rawa. Sai yaron ya fadi yana ta birgima, bakinsa yana kumfa.
And they brought him to him: and when he saw him, immediately the spirit tore him; and he fell on the ground, and wallowed, foaming.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron, Tun yaushe wannan abu ya same shi? Mahaifin yaron ya ce tun yana karami.
And he asked his father, How long is it since this came to him? and he said, From a child.
22 Ya kuwa sha jefa shi a ruwa da wuta, don ya halakar da shi. Idan zaka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimakemu.
And often it hath cast him into the fire, and into the waters to destroy him: but if thou canst do any thing, have compassion on us, and help us.
23 Yesu ya ce masa, “In zan iya? Ai dukan abu mai yiwuwa ne, ga duk wanda ya gaskata.
Jesus said to him, If thou canst believe, all things [are] possible to him that believeth.
24 Nan da nan mahaifin yaron ya daga murya ya ce, Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata.
And immediately the father of the child cried out, and said with tears, Lord, I believe; help thou my unbelief.
25 Da Yesu ya ga taron na dungumowa a guje, sai ya tsawata wa bakin aljanin ya ce masa, “kai, beben aljani na umarce ka, ka fita daga wannan yaron kar ka sake shigar sa.
When Jesus saw that the people came running together, he rebuked the foul spirit, saying to him, [Thou] dumb and deaf spirit, I charge thee, come out of him, and enter no more into him.
26 Sai wannan aljanin ya daga murya ya fita ya rabu da wannan yaron. Sai yaro ya zama kamar mattacce, sai sauran mutanen suka ce, “Ai, yaron ya mutu.
And [the spirit] cried, and rent him severely, and came out of him: and he was as one dead; so that many said, He is dead.
27 Yesu ya kama hannunsa, ya daga shi, sai yaron ya mike tsaye.
But Jesus took him by the hand, and lifted him up; and he arose.
28 Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?”
And when he had come into the house, his disciples asked him privately, Why could not we cast him out?
29 Ya ce masu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”
And he said to them, This kind can come forth by nothing, but by prayer and fasting.
30 Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke.
And they departed thence, and passed through Galilee; and he would not that any man should know [it].
31 Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.
For he taught his disciples, and said to them, The Son of man is delivered into the hands of men, and they will kill him; and after that he is killed, he will rise the third day.
32 Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.
But they understood not that saying, and were afraid to ask him.
33 Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya?
And he came to Capernaum: and being in the house, he asked them, What was it that ye disputed among yourselves by the way?
34 Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma.
But they held their peace: for by the way they had disputed among themselves, who [should be] the greatest.
35 Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.
And he sat down, and called the twelve, and saith to them, If any man desireth to be first, [the same] shall be last of all, and servant of all.
36 Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu.
And he took a child, and set him in the midst of them: and when he had taken him in his arms, he said to them,
37 Dukan wanda ya karbi dan karamin yaron nan a cikin sunana ni ya karba, kuma dukan wanda ya karbi wani, ni ya karba, bai kuma karbeni ni kadai ba, duk da wanda ya aiko ni.”
Whoever shall receive one of such children in my name, receiveth me: and whoever shall receive me, receiveth not me, but him that sent me.
38 Sai Yahaya ya ce masa, Malam mun ga wani yana fitar da aljanu da sunanka mun yi kokari mu hana shi domin ba ya tare da mu.
And John answered him, saying, Master, we saw one casting out demons in thy name, and he followeth not us; and we forbad him, because he followeth not us.
39 Sai Yesu ya ce masu ku kyale shi domin babu wanda zai yi irin wannan babban aikin, sa'annan ya fadi wasu maganganu mara sa kyau a kanmu.
But Jesus said, Forbid him not; for there is no man who shall do a miracle in my name, that can lightly speak evil of me.
40 Duk wanda ba ya gaba da mu, na mu ne.
For he that is not against us, is on our part.
41 Duk wanda ya ba ku ruwa ku sha domin kuna na Almasihu, gaskiya nake fada maku ba za ya rasa ladansa ba.
For whoever shall give you a cup of water to drink in my name, because ye belong to Christ, verily I say to you, he shall not lose his reward.
42 Amma duk wanda ya sa kananan nan tuntube, ya fi kyau a rataya masa dutsen nika a jefa shi a cikin teku.
And whoever shall cause one of [these] little ones that believe in me, to fall into sin, it is better for him that a millstone were hanged about his neck, and he were cast into the sea.
43 Idan har hannun ka zai sa ka yi tuntube, zai fi kyau ka yanke shi. Domin zai fi kyau ka shiga aljanna da hannu daya da ka shiga jahannama da hannu biyu. (Geenna )
And if thy hand causeth thee to fall into sin, cut it off: it is better for thee to enter life maimed, than having two hands to go into hell, into the fire that never shall be quenched: (Geenna )
44 (Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
Where their worm dieth not, and the fire is not quenched.
45 Idan kafarka za ta sa ka yi tuntube, ka yanke ta ka yar. Zai fi kyau ka shiga aljanna da kafa daya da ka shiga jahannama da kafa biyu. (Geenna )
And if thy foot causeth thee to fall into sin, cut it off: it is better for thee to enter halt into life, than having two feet to be cast into hell, into the fire that never shall be quenched: (Geenna )
46 (Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
Where their worm dieth not, and the fire is not quenched.
47 Idan idonka zai sa ka yi tuntube, ka kwakule shi ka yar, domin gwamma ka shiga mulkin Allah da ido daya, da a jefa ka cikin wuta da idanu biyu. (Geenna )
And if thy eye causeth thee to fall into sin, pluck it out: it is better for thee to enter into the kingdom of God with one eye, than having two eyes, to be cast into hell-fire. (Geenna )
48 Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa.
Where their worm dieth not, and the fire is not quenched.
49 Domin da wuta za a tsarkake kowa.
For every one shall be salted with fire, and every sacrifice shall be salted with salt.
50 Gishiri yana da kyau, amma idan ya rasa zakinsa, ta ya ya za ka sa shi yayi zaki kuma? Ku kasance da zaki, kuma ku yi zaman lafiya da kowa.
Salt [is] good: but if the salt hath lost its saltness, with what will ye season it? Have salt in yourselves, and have peace one with another.