< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
V tistih dneh, [ko] je bila množica zelo velika in ni imela nič za jesti, je Jezus poklical k sebi svoje učence in jim rekel:
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
»Sočutje imam do množice, ker so z menoj sedaj že tri dni, pa nimajo ničesar za jesti,
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
in če jih pošljem proč k njihovim lastnim hišam tešče, bodo med potjo oslabeli, kajti številni izmed njih so prišli od daleč.«
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
In njegovi učenci so mu odgovorili: »Od kod lahko človek, tukaj v divjini, te ljudi nasiti s kruhom?«
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
In vprašal jih je: »Koliko hlebov imate?« In rekli so: »Sedem.«
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
In zapovedal je množici, da se usede na tla, in vzel je sedem hlebov ter se zahvalil in prelomil ter dal svojim učencem, da jih postavijo prednje in oni so jih postavili pred množico.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
In imeli so nekaj majhnih rib, in blagoslovil je ter velel, da jih prav tako postavijo pred njih.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
Tako so jedli in bili nasičeni; in od odlomkov hrane, ki je ostala, so pobrali sedem košar.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
In teh, ki so jedli, je bilo okoli štiri tisoč; in poslal jih je proč.
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
In s svojimi učenci je nemudoma vstopil na ladjo ter prišel v dalmanútske kraje.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
In prišli so farizeji, ter se začeli pričkati z njim in ga skušali in od njega iskali znamenje z neba.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
In v svojem duhu je globoko vzdihnil in rekel: »Zakaj ta rod išče znamenje? Resnično, povem vam: ›Temu rodu ne bo dano nobeno znamenje.‹«
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
In zapustil jih je ter vstopil na ladjo in ponovno odplul na drugo stran.
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
Učenci so torej pozabili vzeti kruh niti s seboj na ladji niso imeli več kakor en hleb.
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
In naročil jim je, rekoč: »Pazite, varujte se farizejskega kvasa in Herodovega kvasa.«
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
In med seboj so razpravljali, rekoč: » To je zato, ker nimamo kruha.«
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
Ko je Jezus to spoznal, jim reče: »Zakaj razmišljate, ker nimate kruha? Še niste zaznali niti razumeli? Ali imate svoje srce še vedno zakrknjeno?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
Imate oči, pa ne vidite? Imate ušesa, pa ne slišite? In ali se ne spominjate?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
Ko sem prelomil pet hlebov med pet tisoč, koliko košar, polnih odlomkov, ste pobrali?« Rekli so mu: »Dvanajst.«
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
»In ko sedem med štiri tisoč, koliko košar, polnih odlomkov, ste pobrali?« In rekli so: »Sedem.«
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
In rekel jim je: »Kako to, da ne razumete?«
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
In pride v Betsajdo, in k njemu privedejo slepega moža in rotili so ga, da se ga dotakne.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
In z roko je prijel slepega moža in ga odvedel iz mesta in ko je pljunil na njegove oči in svoji roki položil nanj, ga je vprašal, ali karkoli vidi.
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
In ta je pogledal gor ter rekel: »Vidim ljudi kakor drevesa, hodijo.«
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Nató je svoje roke ponovno položil na njegove oči in ga pripravil, da pogleda gor, in bil je ozdravljen in razločno videl vsakega človeka.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
In poslal ga je proč k njegovi hiši, rekoč: »Niti ne pojdi v mesto niti tega ne povej nikomur v mestu.«
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
In Jezus je odšel ven ter njegovi učenci, v mesta Cezareje Filipove. Med potjo pa je svoje učence vprašal, rekoč jim: »Kdo ljudje pravijo, da sem jaz?«
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
Odgovorili so: »Janez Krstnik, « toda nekateri pravijo »Elija, « drugi pa: »Eden izmed prerokov.«
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
In reče jim: »Toda kdo vi pravite, da sem jaz?« In Peter odgovori ter mu reče: »Ti si Kristus.«
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
In naročil jim je, da naj nobenemu človeku ne povedo o njem.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
In začel jih je učiti, da mora Sin človekov pretrpeti mnoge stvari in biti zavrnjen od starešin in od visokih duhovnikov in pisarjev in biti ubit ter po treh dneh ponovno vstati.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
In ta govor je govoril javno. Peter pa ga je prijel in ga začel oštevati.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
Toda ko se je obrnil okoli in pogledal na svoje učence, je Petra oštel, rekoč: »Spravi se za menoj, Satan, kajti ne posvečaš se stvarem, ki so Božje, temveč stvarem, ki so od ljudi.«
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
In ko je k sebi poklical množico, skupaj s svojimi učenci, jim je rekel: »Kdorkoli hoče priti za menoj, naj se odpove samemu sebi in vzame svoj križ in mi sledi.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
Kajti kdorkoli hoče rešiti svoje življenje, ga bo izgubil, toda kdorkoli bo izgubil svoje življenje zaradi mene in evangelija, ta isti ga bo rešil.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
Kajti kaj bo koristilo človeku, če bo pridobil ves svet, izgubil pa svojo lastno dušo?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
Ali kaj bo dal človek v zamenjavo za svojo dušo?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
Kdorkoli se bo torej v tem zakonolomnem in grešnem rodu sramoval mene in mojih besed, tega se bo sramoval tudi Sin človekov, ko pride v slavi svojega Očeta s svetimi angeli.«

< Markus 8 >