< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
BUT in those days when the multitude was great and there was nothing for them to eat, he called his disciples, and said to them,
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
I have compassion on this multitude, for behold three days have they continued with me, and there is nothing which they may eat.
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
And if it be that I send them away fasting to their houses, they will faint in the way; for some of them come from afar.
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
His disciples say to him, Whence can any one here in the wilderness satisfy with bread all these?
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
And he asked them, How many loaves have you? They say to him, Seven;
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
and he directed the multitudes to recline upon the ground, and he took those seven loaves, and blessed and brake and gave to his disciples that they should set, and they set before the assemblies.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
And there were fishes, a few: and also over them he blessed, and said that they should set them.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
And they all ate and were satisfied, and took up the abundancies of the fragments, seven panniers.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
Now the men who had eaten were about four thousand: and he dismissed them,
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
and immediately ascended into a vessel with his disciples, and came to the region of Dalmanutha.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
AND there came forth Pharishee, and began to question with him, and they demanded of him the sign from heaven, tempting him.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
And he groaned in his spirit, and said, Why seeketh this generation the sign? Amen I say to you, There shall not be given the sign unto this generation.
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
And he left them, and ascended into the ship, and went to that overland.
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
And they had forgotten to take with them bread, and but one cake was with them in the ship.
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
And he counselled them, and said to them, Look and beware of the leaven of the Pharishee, and of the leaven of Herodes.
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
And they reasoned one with another, saying, Because we have no bread.
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
But Jeshu knew, and said to them, Why reason you because you have no bread? do you not yet know nor under stand? is your heart still hard?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
and eyes have you, and not see? and ears have you, and not hear? neither remember you?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
When those five loaves I brake to five thousand, how many baskets full of fragments did you take up? They said to him, Twelve.
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
He saith to them. And when seven to four thousand, how many panniers of fragments when filled took you up? They say, Seven.
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
He saith to them, How do you not yet understand?
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
And he came to Beth-tsaida; and they brought to him a blind man, and prayed of him to touch him.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
And he took the hand of the blind man, and led him forth without from the village; and spat in his eyes, and laid (on them) his hand, and inquired whether he saw.
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
And he looked, and said, I see the sons of man as the trees, walking.
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Again he laid his hand upon his eyes, and he was restored, and he saw every thing clearly.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
And he sent him to his house, and told him to go not into the village, nor to inform any man in the village.
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
And Jeshu went forth and his disciples into the villages of Kesarea of Philipos, and he interrogated his disciples by the way, saying to them, What say men concerning me that I am?
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
But they answered, That (thou art) Juchanon the Baptizer; and others, that (thou art) Elia; and others, one from the prophets.
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
Jeshu said to them, But you, what say you concerning me that I am? Shemun Kipha answered and said to him, Thus art the Meshicha, the Son of Aloha the Living.
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
And he charged them that to any one they should not tell concerning him.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
And he began to teach them, that it was to be that the Son of man should suffer much, and be rejected by the elders, and by the chief priests, and by the Sophree, and be killed, and that the third day he should arise!
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
And he spake the word with them fully. And Kipha took him, and began to chide him.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
But he turned, and, beholding his disciples, reprehended Shemun, and said, Get thee behind me, Satana, for thou thinkest not that which is of Aloha, but that which is of the sons of men.
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
AND Jeshu called to the assemblies with his disciples, and said to them, Whoever will come after me, let him deny himself, and take up his cross, and come after me.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
For every one who willeth to save his life shall lose it; and every one who shall lose his life on account of me and on account of my gospel, shall save it.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
For what is a man profited, if the whole world he gain, and his soul be lost?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
Or what shall a son of man give (as) the compensation for his soul?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
For whoever shall be ashamed of me and of my words in this generation, sinful and adulterous, the Son of man will also be ashamed of him, when he cometh in the glory of his Father with the holy angels.

< Markus 8 >