< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
In those days when a large crowd had again assembled and had nothing to eat, Jesus called together his disciples and said to them.
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
"My heart aches for the crowd, because they have remained with me three days now, and they have nothing to eat;
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
and if I send them away fasting to their homes, they will faint on the way. Moreover, some of them are from a distance."
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
"Where will it be possible," answered his disciples, "for one to fill these men with bread in a lonely place like this?"
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
He asked them, "How many loaves have you?" "Seven," they said.
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
So he directed the crowd to sit down on the ground; and when he had taken the seven loaves, he gave thanks, broke them, and gave to his disciples to distribute to the crowd.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
They had also a few small fish; after blessing these he told his disciples to distribute them also.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
They ate and were filled and they took up of broken pieces that were left, seven hampers.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
They that had eaten were about four thousand.
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
Then he sent them away, got at once into the boat with his disciples. and came into the district of Dalmanutha.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
And the Pharisees came out and began to question him, seeking from him a sign from heaven, by way of testing him.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
At this Jesus sighed deeply in his spirit, and said. "Why does the present generation seek a sign? In solemn truth I tell you that no sign shall be given this generation."
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
Then he left them, and getting into the boat again, went away to the other side,
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
Now they had forgotten to take bread, and had not in the boat with them more than one loaf.
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
So he gave them this warning. "Look out! Be on the watch against the leaven of the Pharisees, and the leaven of Herod."
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
And they began arguing with one another because they had no bread, He noted this and said to them.
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
"Why are you arguing together because you have no bread? Do you not yet perceive and understand?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
Are your minds so slow to comprehend? You have eyes, do you not see? You have ears, do you not hear?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
Do you not remember? When I broke the five loaves among the five thousand, how many baskets of broken pieces did you take up?" "Twelve," they said.
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
"And when the seven for the four thousand, how many hampers full of fragments did you pick up?"
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
"Do you not yet understand?" he said.
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
Then they came to Bethsaida, where some people brought a blind man to Jesus, and begged him to touch him.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
Taking the blind man by the hand, he led him outside the village; and, after spitting on his eyes, he laid his hands on him and asked, "Can you make out anything?"
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
The man looked up and said, "I can make out the people, for as they move about, I see them like trees."
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Then Jesus again put his hands on the man’s eyes; and the man, staring straight ahead, recovered his sight and continued to see everything perfectly.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
Then Jesus sent him home, saying, "Do not even go into the village."
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
From there Jesus and his disciples went to the villages of Caesarea Philippi, and on the way he began to question his disciples saying, "Who do people say I am?"
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
And they told him. "Some say Johnthe Baptist, others, Elijah, and others that you are one of the prophets."
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
And he continued questioning them, "But you yourselves, Who do you say I am?" Peter in reply said to him, "You are Christ."
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
Then he strictly charged them not to say this about him to any one;
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
and he began to explain to them that the Son of man must suffer many things, and be rejected by the elders and the chief priests, and the Scribes, and be put to death, and after two days rise again.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
This he told them quite openly. Then Peter took him and began to rebuke him.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
But he turned round, and looked upon his disciples, and rebuked Peter. "Get thee behind me, Satan," he said, "for your thoughts are not God’s thoughts, but man’s."
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
Then summoning the crowd to him, with his disciples. he said. "If any man wishes to follow me, let him renounce self, take up his cross, and so follow me.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
For whoever wishes to save his life will lose it; but whoever, for my sake and the gospel’s, loses his life will save it.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
For what shall it profit a man to gain the whole world and lose his own life?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
Or what shall a man give in exchange for his life?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
Whoever is ashamed of me and my words in this unfaithful and wicked generation, of him shall the Son of man be ashamed when he comes in the glory of his Father with the holy angels."

< Markus 8 >