< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
In those days, the multitude being large, and having nothing which they may eat, Jesus calling His disciples, says to them,
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
I sympathize with the multitude because three days already abide unto me, and they have nothing which they may eat.
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
If I shall send them away to their homes fasting, they will faint on the road; indeed some of them have come from afar.
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
And His disciples responded, Whence shall any one be able to feed these with bread in the desert?
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
And He asked them, How much bread have you? And they said, Seven loaves.
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
He commanded the multitude to sit down on the ground; and taking the seven loaves, giving thanks, He broke, and gave them to His disciples, that they may dispense them; and they presented them to the multitude.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
And they had a few fishes: and blessing them, He delivered them.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
And they ate, and were filled: and they took up the residue of the fragments, seven baskets.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
And those eating were about four thousand. And He sent them away.
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
And immediately having gone into the ship with His disciples, He came to the parts of Dalmanutha.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
And the Pharisees came out, and began to question Him, seeking from Him a sign from heaven. tempting Him.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
And groaning in spirit, He says, What sign does this generation seek after? truly I say unto you, No sign shall be given unto this generation.
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
And having left them, coming in again He departed to the other side.
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
And they forgot to take bread; and had but one loaf with them in the ship.
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
And He commanded them, saying, See, beware of the leaven of the Pharisees, and of the leaven of Herod.
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
And they were reasoning to one another, saying, It is because we have not bread.
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
And Jesus knowing says to them, Why do you reason because you have not bread? do you not yet know, nor understand? have you your heart still hardened?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
Having eyes, do you not see? having ears, do you not hear? and do you not remember?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
When I broke the five loaves to the five thousand, how many baskets full of fragments did you take up? They say to Him, Twelve.
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
And when the seven loaves to the four thousand, how many baskets full of fragments did you take up? And they said, Seven.
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
And He said to them, Do you not yet understand?
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
And they come into Bethsaida: and they bring Him a blind man, and they intreat Him that He may touch him.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
And taking the blind man by the hand, He led him out of the village; and spitting in his eyes, putting His hands on him, He asked him, if he sees anything.
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
And looking up he said, I see the men walking about like trees.
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Then again He put His hands on his eyes, and he looked up; and was restored, and saw all things distinctly.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
And He sent him to his own house, saying, Go not into the village.
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
And Jesus and His disciples went away into the villages of Caesarea Philippi; and on the way He asked His disciples, saying to them, Whom do the people say that I am?
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
And they answered Him saying, John the Baptist: and others, Elijah; and others, One of the prophets.
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
And He asked them, Whom do you say that I am? And Peter responding says to Him, Thou art the Christ.
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
And He charged them that they should speak to no one concerning Him.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
And He began to teach them, that it behooves the Son of man to suffer many things, and to be rejected by the elders, and the chief priests and the scribes, and to be killed, and after three days to rise.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
And He was boldly speaking the word. And Peter taking Him to him began to rebuke Him.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
And He turning and seeing His disciples rebuked Peter, and says, Get behind me, adversary: because thou art not thinking the things of God, but those of men.
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
And calling the multitude to Him with His disciples, He said to them, Whosoever wishes to come after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
For whosoever may wish to save his soul shall lose it; and whosoever shall lose his soul for my sake and that of the gospel shall save it.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
For what shall it profit a man to gain the whole world, and lose his own soul?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
For what would a man give in exchange for his soul?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
For whosoever may be ashamed of me and my words in this adulterous and wicked generation, the Son of man shall also be ashamed of him, when He may come in the glory of His Father with the holy angels.

< Markus 8 >