< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
In those days, the multitude being very large and not having anything to eat, Jesus called His disciples and said to them:
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
“I have compassion on the multitude, because they have stayed with me three days now and have nothing to eat.
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
If I send them away hungry to their homes, they will give out on the way, because some of them have come a long distance.”
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
His disciples answered Him, “From what source could anyone satisfy these people with bread here in a wilderness?”
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
He asked them, “How many loaves do you have?” And they said, “Seven.”
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
So He told the crowd to sit down on the ground; then taking the seven loaves and giving thanks, He broke them and gave them to His disciples to set before the crowd, and they did.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
They also had a few small fish; so blessing them He said to distribute them as well.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
Well they ate and were filled; they even took up seven hampers of broken pieces that were left over.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
Now those who had eaten were about four thousand; and He sent them away.
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
Then He got right into the boat with His disciples and went to the region of Dalmanutha.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
The Pharisees came out and began to argue with Him, requesting of Him a sign from heaven, by way of testing Him.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
But He sighed deeply in His spirit and said: “Why does this generation seek a sign? I tell you emphatically, no sign shall be given to this generation!”
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
Turning His back on them, He got back into the boat and went off to the other side.
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
(His disciples had forgotten to take bread; they did not have more than one loaf with them in the boat.)
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
And He charged them, saying, “Watch out; beware of the leaven of the Pharisees and the leaven of Herod.”
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
So they started reasoning among themselves, saying, “It's because we have no bread.”
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
Being aware of it Jesus said to them: “Why are you reasoning because you have no bread? Do you still neither perceive nor understand? Do you still have hearts that have been hardened?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
Having eyes do you not see, and having ears do you not hear, and do you not remember?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
When I broke the five loaves for the five thousand, how many baskets full of pieces did you take up?” They say to Him, “Twelve.”
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
“And when I broke the seven for the four thousand, how many hampers full of pieces did you take up?” And they said, “Seven.”
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
So He said to them, “How is it that you still don't understand?”
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
Then He came to Bethsaida; and they brought a blind man to Him and begged Him to touch him.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
So He took the blind man by the hand and led him out of the village; then spitting into his eyes and laying hands on him, He asked him if he saw anything.
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
And looking up he said, “I do see men, only they look like walking trees.”
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Then He put His hands on his eyes again, and made him look up; and he was restored and saw everyone clearly.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
Then He sent him away to his house, saying, “Neither go into the village nor tell anyone in the village.”
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
Then Jesus and His disciples set out for the towns of Caesarea Philippi; and on the way He questioned His disciples, saying to them, “Who are people saying that I am?”
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
So they answered, “John the Baptist; others Elijah; still others one of the prophets.”
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
He said to them, “And who do you say that I am?” So Peter answered and said to Him, “You are the Christ!”
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
Then He charged them that they should tell no one about Him.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
He then began to teach them that the Son of the Man must suffer many things, and be rejected by the elders, chief priests and the scribes, and be killed, and after three days rise again.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
He said these things quite plainly. Then Peter took Him aside and began to rebuke Him.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
But He turned, looked at His disciples, and rebuked Peter, saying: “Get behind me, Satan! You have in mind men's values, not God's values.”
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
He summoned the crowd, along with His disciples, and said to them: “Whoever wants to follow along behind me must deny himself and take up his cross and follow me.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
Because whoever may resolve to ‘save’ his life will waste it; but whoever may ‘waste’ his life for my sake and the Gospel's, he will save it.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
Well, what will it profit a man if he gains the whole world, yet forfeits his soul?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
Or what can a man give in exchange for his soul?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
Yes, whoever is ashamed of me and my words in this adulterous and sinful generation, the Son of the Man will also be ashamed of Him whenever He comes in the glory of His Father with the holy Angels.”

< Markus 8 >