< Markus 8 >

1 A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
In those days, the multitude being very great, and having nothing to eat, Jesus called his disciples to him and said to them:
2 “Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
I have compassion on the multitude, because they have continued with me now three days, and have nothing to eat.
3 Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
And if I send them home fasting, they will faint on the way; for some of them have come from afar.
4 Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
And his disciples answered him: Whence will any one be able to satisfy these men with bread, here in the wilderness?
5 Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
And he asked them: How many loaves have you? And they said: Seven.
6 Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
And he commanded the multitude to recline on the ground. And he took the seven loaves, and gave thanks, and broke them, and gave them to the disciples to set before them: and they set them before the multitude.
7 Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
And they had a few small fishes; and he blessed, and commanded that they also be set before them.
8 Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
And they ate, and were satisfied; and they took up what remained of the broken pieces, seven baskets.
9 Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
And those who had eaten were about four thousand; and he sent them away.
10 Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
And he immediately entered the ship with his disciples, and went into the regions of Dalmanutha.
11 Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
And the Pharisees came out, and began to put questions to him, asking of him a sign from heaven, that they might tempt him.
12 Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
And he sighed deeply in his spirit, and said: Why does this generation seek for a sign? Verily I say to you, No sign will be given to this generation.
13 Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
And he left them, and entered the ship again, and departed to the opposite side.
14 A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
And they had forgotten to take bread; and they had but one loaf with them in the ship.
15 Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
And he charged them, saying: Take heed, and beware of the leaven of the Pharisees, and of the leaven of Herod.
16 Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
And they reasoned with one another, saying: It is because we have no bread.
17 Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
And Jesus perceived it, and said to them: Why do you reason, because you have no bread? Do you not yet perceive, nor understand? Is your heart still hardened?
18 Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
Having eyes, do you not see? and having ears, do you not hear? and do you not remember?
19 Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
When I broke the five loaves among the five thousand, how many baskets full of broken pieces did you take up? They said to him: Twelve.
20 Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
When I broke the seven among the four thousand, how many baskets full of broken pieces did you take up? They replied: Seven.
21 Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
And he said to them: How is it that you do not understand?
22 Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
And he came to Bethsaida; and they brought to him a blind man, and besought him to touch him.
23 Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
And he took the blind man by the hand, and led him out of the village. And he spit on his eyes, and laid his hands on him, and asked him if he saw any thing.
24 Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
And he looked up and said: I see men, like trees, walking.
25 Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
Then he again laid his hands on his eyes, and made him look up. And he was restored, and saw all things clearly.
26 Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
And he sent him away to his house, and said: Neither go into the village, nor tell it to any one in the village.
27 Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
And Jesus and his disciples went out into the villages of Cæsarea Philippi. And on the road, he asked his disciples, saying to them: Who do men say that I am?
28 Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
They answered: John the Immerser; and others, Elijah; and others, one of the prophets.
29 Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
And he said to them: But who say you that I am? Peter answered and said to him: Thou art the Christ.
30 Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
And he charged them to tell no one concerning him.
31 Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
And he began to teach them, that the Son of man must suffer many things, and be rejected by the elders, and the chief priests, and the scribes, and be put to death, and after three days rise again.
32 Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
And he spoke this saying plainly. And Peter took him aside and began to rebuke him.
33 Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
But he turned about, and, looking on his disciples, rebuked Peter, saying: Get behind me, adversary: for you are not thinking of the things of God, but of the things of men.
34 Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
And he called to him the multitude with his disciples, and said to them: Whoever determines to follow after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me.
35 Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
For whoever will save his life, shall lose it; but whoever will lose his life for my sake and the gospel’s, shall save it.
36 Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
For what will it profit a man, if he gain the whole world, and lose his own life?
37 Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
Or, what will a man give as a ransom for his life?
38 Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”
For whoever will be ashamed of me, and my words, in this sinful and adulterous generation, of him the Son of man also will be ashamed, when he comes in the glory of his Father, with the holy angels.

< Markus 8 >