< Markus 7 >
1 Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.
Og Farisæerne og nogle af de skriftkloge, som vare komne fra Jerusalem, samle sig om ham.
2 Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba,
Og da de så nogle af hans Disciple holde Måltid med vanhellige, det er utoede, Hænder
3 (Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa.
thi Farisæerne og alle Jøderne spise ikke uden at to Hænderne omhyggeligt, idet de fastholde de gamles Overlevering;
4 Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
og når de komme fra Torvet, spise de ikke uden først at tvætte sig; og der er mange andre Ting, som de have vedtaget at holde, Tvætninger af Bægere og Krus og Kobberkar og Bænke,
5 Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, “Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?”
så spurgte Farisæerne og de skriftkloge ham ad: "Hvorfor vandre dine Disciple ikke efter de gamles Overlevering, men holde Måltid med vanhellige Hænder?"
6 Amma ya amsa masu cewa, “Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni.
Men han sagde til dem: "Rettelig profeterede Esajas om eder, I Hyklere! som der er skrevet: "Dette Folk ærer mig med Læberne, men deres Hjerte er langt borte fra mig.
7 Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'”.
Men de dyrke mig forgæves, idet de lære Lærdomme, som ere Menneskers Bud."
8 Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane.
I forlade Guds Bud og holde Menneskers Overlevering."
9 Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane.
Og han sagde til dem: "Smukt ophæve I Guds Bud, for at I kunne holde eders Overlevering.
10 Koda shike Musa ya rubuta cewa, “ka girmama Ubanka da Uwarka”, kuma, “duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take”.
Thi Moses har sagt: "Ær din Fader og din Moder"; og:"Den, som hader Fader eller Moder, skal visselig dø".
11 Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, “duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)”'.
Men I sige: Når en Mand siger til sin Fader eller sin Moder: "Det, hvormed du skulde være hjulpen af mig, skal være Korban (det er: Tempelgave),"
12 Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu.
da tilstede I ham ikke mere at gøre noget for sin Fader eller Moder,
13 Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi.”
idet I ophæve Guds Ord ved eders Overlevering, som I have overleveret; og mange lignende Ting gøre I."
14 Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, “ku kasa kunne gareni, kuma ku gane.
Og han kaldte atter Folkeskaren til sig og sagde til dem: "Hører mig alle, og forstår!
15 Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi”
Der er intet uden for Mennesket, som, når det går ind i ham, kan gøre ham uren; men hvad der går ud af Mennesket, det er det, som gør Mennesket urent.
16 Bari mai kunnen ji, ya ji.
Dersom nogen har Øren at høre med, han høre!"
17 Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali.
Og da han var gået ind i Huset og var borte fra Skaren, spurgte hans Disciple ham om Lignelsen.
18 Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba,
Og han siger til dem: "Ere også I så uforstandige? Forstå I ikke, at intet, som udefra går ind i Mennesket, kan gøre ham uren?
19 domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga”. Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
Thi det går ikke ind i hans Hjerte men i hans Bug og går ud ad den naturlige Vej, og således renses al Maden."
20 Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi
Men han sagde: "Det, som går ud af Mennesket, dette gør Mennesket urent.
21 Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa,
Thi indvortes fra, fra Menneskenes Hjerte, udgå de onde Tanker, Utugt, Tyveri, Mord,
22 zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci.
Hor, Havesyge, Ondskab, Svig, Uterlighed, et ondt Øje, Forhånelse, Hovmod, Fremfusenhed;
23 Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi.”
alle disse onde Ting udgå indvortes fra og gøre Mennesket urent."
24 Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba.
Og han stod op og gik bort derfra til Tyrus's og Sidons Egne. Og han gik ind i et Hus og vilde ikke, at nogen skulde vide det. Og han kunde dog ikke være skjult;
25 Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa.
men en Kvinde, hvis lille Datter havde en uren Ånd, havde hørt om ham og kom straks ind og faldt ned for hans Fødder;
26 Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
(men Kvinden var græsk, af Herkomst en Syrofønikerinde), og hun bad ham om, at han vilde uddrive den onde Ånd af hendes Datter.
27 Sai ya ce mata, “Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba”.
Og han sagde til hende: "Lad først Børnene mættes; thi det er ikke smukt at tage Børnenes Brød og kaste det for de små Hunde."
28 Sai ta amsa masa cewa, “I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan.”
Men hun svarede og siger til ham: "Jo, Herre! også de små Hunde æde under Bordet af Børnenes Smuler."
29 Ya ce mata, “domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki.”
Og han sagde til hende: "For dette Ords Skyld gå bort; den onde Ånd er udfaren af din Datter"
30 Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
Og hun gik bort til sit Hus og fandt Barnet liggende på Sengen og den onde Ånd udfaren.
31 Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis.
Og da han gik bort igen fra Tyrus's Egne, kom han over Sidon midt igennem Dekapolis's Egne til Galilæas Sø.
32 Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
Og de bringe ham en døv, som også vanskeligt kunde tale, og bede ham om, at han vilde lægge Hånden på ham.
33 Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa.
Og han tog ham afsides fra Skaren og lagde sine Fingre i hans Øren og spyttede og rørte ved hans Tunge
34 Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, “Ifatha”, wato, “bude!”
og så op til Himmelen, sukkede og sagde til ham: "Effata!" det er: lad dig op!
35 Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
Og hans Øren åbnedes, og straks løstes hans Tunges Bånd, og han talte ret.
36 Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina.
Og han bød dem, at de ikke måtte sige det til nogen; men jo mere han bød dem, desto mere kundgjorde de det.
37 kuma suna ta mamaki cewa, “Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana.”
Og de bleve over al Måde slagne af Forundring og sagde: "Han har gjort alle Ting vel; både gør han, at de døve høre, og at målløse tale."