< Markus 6 >

1 Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
Jesus went on from there and came to His hometown, accompanied by His disciples.
2 Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
When the Sabbath came, He began to teach in the synagogue, and many who heard Him were astonished. “Where did this man get these ideas?” they asked. “What is this wisdom He has been given? And how can He perform such miracles?
3 Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
Isn’t this the carpenter, the son of Mary and the brother of James, Joses, Judas, and Simon? Aren’t His sisters here with us as well?” And they took offense at Him.
4 Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
Then Jesus said to them, “Only in his hometown, among his relatives, and in his own household is a prophet without honor.”
5 Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
So He could not perform any miracles there, except to lay His hands on a few of the sick and heal them.
6 Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
And He was amazed at their unbelief. And He went around from village to village, teaching the people.
7 Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
Then Jesus called the Twelve to Him and began to send them out two by two, giving them authority over unclean spirits.
8 ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
He instructed them to take nothing but a staff for the journey—no bread, no bag, no money in their belts—
9 sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
and to wear sandals, but not a second tunic.
10 Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
And He told them, “When you enter a house, stay there until you leave that area.
11 Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
If anyone will not welcome you or listen to you, shake the dust off your feet when you leave that place, as a testimony against them.”
12 Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
So they set out and preached that the people should repent.
13 Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
They also drove out many demons and healed many of the sick, anointing them with oil.
14 Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
Now King Herod heard about this, for Jesus’ name had become well known, and people were saying, “John the Baptist has risen from the dead! That is why miraculous powers are at work in him.”
15 Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
Others were saying, “He is Elijah,” and still others, “He is a prophet, like one of the prophets of old.”
16 Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
But when Herod heard this, he said, “John, whom I beheaded, has risen from the dead!”
17 Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
For Herod himself had ordered that John be arrested and bound and imprisoned, on account of his brother Philip’s wife Herodias, whom Herod had married.
18 Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
For John had been telling Herod, “It is not lawful for you to have your brother’s wife!”
19 Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
So Herodias held a grudge against John and wanted to kill him. But she had been unable,
20 Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
because Herod feared John and protected him, knowing that he was a righteous and holy man. When he heard John’s words, he was greatly perplexed; yet he listened to him gladly.
21 Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
On Herod’s birthday, her opportunity arose. Herod held a banquet for his nobles and military commanders and the leading men of Galilee.
22 Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
When the daughter of Herodias came and danced, she pleased Herod and his guests, and the king said to the girl, “Ask me for whatever you wish, and I will give it to you.”
23 Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
And he swore to her, “Whatever you ask of me, I will give you, up to half my kingdom!”
24 Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
Then she went out and asked her mother, “What should I request?” And her mother answered, “The head of John the Baptist.”
25 Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
At once the girl hurried back to the king with her request: “I want you to give me the head of John the Baptist on a platter immediately.”
26 Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
The king was consumed with sorrow, but because of his oaths and his guests, he did not want to refuse her.
27 Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
So without delay, the king commanded that John’s head be brought in. He sent an executioner, who went and beheaded him in the prison.
28 Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
The man brought John’s head on a platter and presented it to the girl, who gave it to her mother.
29 Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
When John’s disciples heard about this, they came and took his body and placed it in a tomb.
30 Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
Meanwhile, the apostles gathered around Jesus and brought Him news of all they had done and taught.
31 Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
And He said to them, “Come with Me privately to a solitary place, and let us rest for a while.” For many people were coming and going, and they did not even have time to eat.
32 Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
So they went away in a boat by themselves to a solitary place.
33 Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
But many people saw them leaving and recognized them. They ran together on foot from all the towns and arrived before them.
34 Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
When Jesus stepped ashore and saw a large crowd, He had compassion on them, because they were like sheep without a shepherd. And He began to teach them many things.
35 Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
By now the hour was already late. So the disciples came to Jesus and said, “This is a desolate place, and the hour is already late.
36 Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
Dismiss the crowd so they can go to the surrounding countryside and villages and buy themselves something to eat.”
37 Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
But Jesus told them, “You give them something to eat.” They asked Him, “Should we go out and spend two hundred denarii to give all of them bread to eat?”
38 Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
“Go and see how many loaves you have,” He told them. And after checking, they said, “Five—and two fish.”
39 Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
Then Jesus directed them to have the people sit in groups on the green grass.
40 Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
So they sat down in groups of hundreds and fifties.
41 Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
Taking the five loaves and the two fish and looking up to heaven, Jesus spoke a blessing and broke the loaves. Then He gave them to His disciples to set before the people. And He divided the two fish among them all.
42 Dukansu suka ci suka koshi.
They all ate and were satisfied,
43 Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
and the disciples picked up twelve basketfuls of broken pieces of bread and fish.
44 Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
And there were five thousand men who had eaten the loaves.
45 Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
Immediately Jesus made His disciples get into the boat and go on ahead of Him to Bethsaida, while He dismissed the crowd.
46 Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
After bidding them farewell, He went up on the mountain to pray.
47 Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
When evening came, the boat was in the middle of the sea, and Jesus was alone on land.
48 Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
He could see that the disciples were straining to row, because the wind was against them. About the fourth watch of the night, Jesus went out to them, walking on the sea. He intended to pass by them,
49 Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
but when they saw Him walking on the sea, they cried out, thinking He was a ghost—
50 gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
for they all saw Him and were terrified. But Jesus spoke up at once: “Take courage! It is I. Do not be afraid.”
51 Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
Then He climbed into the boat with them, and the wind died down. And the disciples were utterly astounded,
52 Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
for they had not understood about the loaves, but their hearts had been hardened.
53 Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
When they had crossed over, they landed at Gennesaret and moored the boat.
54 Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
As soon as they got out of the boat, the people recognized Jesus
55 Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
and ran through that whole region, carrying the sick on mats to wherever they heard He was.
56 Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.
And wherever He went—villages and towns and countrysides—they laid the sick in the marketplaces and begged Him just to let them touch the fringe of His cloak. And all who touched Him were healed.

< Markus 6 >