< Markus 6 >

1 Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
Og han gik bort derfra. Og han kommer til sin Fædreneby, og hans Disciple følge ham.
2 Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
Og da det blev Sabbat, begyndte han at lære i Synagogen, og de mange, som hørte ham, bleve slagne af Forundring og sagde: „Hvorfra har han dog dette, og hvad er det for en Visdom, som er given ham, og hvilke kraftige Gerninger der dog sker ved hans Hænder!
3 Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
Er denne ikke Tømmermanden, Marias Søn og Jakobs og Joses's og Judas's og Simons Broder? Og ere ikke hans Søstre her hos os?” Og de forargedes paa ham.
4 Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
Og Jesus sagde til dem: „En Profet er ikke foragtet uden i sit eget Fædreland og iblandt sine Slægtninge og i sit Hus.”
5 Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
Og han kunde ikke gøre nogen kraftig Gerning der; kun lagde han Hænderne paa nogle faa syge og helbredte dem.
6 Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
Og han forundrede sig over deres Vantro. Og han gik om i Landsbyerne der omkring og lærte.
7 Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
Og han hidkalder de tolv, og han begyndte at udsende dem, to og to, og gav dem Magt over de urene Aander.
8 ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
Og han bød dem, at de skulde intet tage med paa Vejen uden en Stav alene, ikke Brød, ikke Taske, ikke Kobber i Bæltet,
9 sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
men have Sko paa og: „Ifører eder ikke to Kjortler!”
10 Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
Og han sagde til dem: „Hvor I komme ind i et Hus, der skulle I blive, indtil I drage bort fra Stedet.
11 Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
Og hvor man ikke vil modtage eder og ikke vil høre eder, der skulle I gaa bort fra og afryste Støvet under eders Fødder til Vidnesbyrd imod dem.”
12 Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
Og de gik ud og prædikede, at man skulde omvende sig.
13 Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
Og de dreve onde Aander ud og salvede mange syge med Olie og helbredte dem.
14 Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
Og Kong Herodes hørte det (thi hans Navn var blevet bekendt), og han sagde: „Johannes Døberen er oprejst fra de døde, og derfor virke Kræfterne i ham.”
15 Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
Andre sagde: „Det er Elias;” men andre sagde: „Det er en Profet ligesom en af Profeterne.”
16 Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
Men da Herodes hørte det, sagde han: „Johannes, som jeg har ladet halshugge, han er oprejst.”
17 Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
Thi Herodes havde selv sendt Bud og ladet Johannes gribe og kaste i Fængsel for sin Broder Filips Hustru, Herodias's Skyld; thi han havde taget hende til Ægte.
18 Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
Johannes sagde nemlig til Herodes: „Det er dig ikke tilladt at have din Broders Hustru.”
19 Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
Men Herodias bar Nag til ham og vilde gerne slaa ham ihjel, og hun kunde det ikke.
20 Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
Thi Herodes frygtede for Johannes, fordi han vidste, at han var en retfærdig og hellig Mand, og han holdt sin Haand over ham; og naar han hørte ham, var han tvivlraadig om mange Ting, og han hørte ham gerne.
21 Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
Og da der kom en belejlig Dag, da Herodes paa sin Fødselsdag gjorde et Gæstebud for sine Stormænd og Krigsøversterne og de ypperste i Galilæa,
22 Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
og da selve Herodias's Datter kom ind og dansede, behagede hun Herodes og Gæsterne. Og Kongen sagde til Pigen: „Bed mig, om hvad som helst du vil, saa vil jeg give dig det.”
23 Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
Og han svor hende til og sagde: „Hvad som helst du beder om, vil jeg give dig, indtil Halvdelen af mit Rige.”
24 Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
Og hun gik ud og sagde til sin Moder: „Hvad skal jeg bede om?” Men hun sagde: „Om Johannes Døberens Hoved.”
25 Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
Og hun gik straks skyndsomt ind til Kongen, bad og sagde: „Jeg vil, at du straks giver mig Johannes Døberens Hoved paa et Fad.”
26 Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
Og om end Kongen blev meget bedrøvet, vilde han dog for Edernes og Gæsternes Skyld ikke afvise hende.
27 Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
Og Kongen sendte straks en af Vagten og befalede at bringe hans Hoved.
28 Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
Og denne gik hen og halshuggede ham i Fængselet; og han bragte hans Hoved paa et Fad og gav det til Pigen, og Pigen gav det til sin Moder.
29 Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
Og da hans Disciple hørte det, kom de og toge hans Lig og lagde det i en Grav.
30 Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
Og Apostlene samle sig om Jesus, og de forkyndte ham alt, hvad de havde gjort, og hvad de havde lært.
31 Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
Og han siger til dem: „Kommer nu I med afsides til et øde Sted og hviler eder lidt;” thi der var mange, som gik til og fra, og de havde ikke engang Ro til at spise.
32 Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
Og de droge bort i Skibet til et øde Sted afsides.
33 Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
Og man saa dem drage bort, og mange kendte dem, og til Fods strømmede de sammen derhen fra alle Byerne og kom før end de.
34 Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
Og da han gik i Land, saa han en stor Skare, og han ynkedes inderligt over dem; thi de vare som Faar, der ikke have Hyrde; og han begyndte at lære dem meget.
35 Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
Og da Tiden allerede var fremrykket, kom hans Disciple til ham og sagde: „Stedet er øde, og Tiden er allerede fremrykket.
36 Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
Lad dem gaa bort, for at de kunne gaa hen i de omliggende Gaarde og Landsbyer og købe sig noget at spise.”
37 Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
Men han svarede og sagde til dem: „Giver I dem at spise!” Og de sige til ham: „Skulle vi gaa hen og købe Brød for to Hundrede Denarer og give dem at spise?”
38 Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
Men han siger til dem: „Hvor mange Brød have I? Gaar hen og ser efter!” Og da de havde faaet det at vide, sige de: „Fem, og to Fisk.”
39 Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
Og han bød dem at lade dem alle sætte sig ned i smaa Flokke i det grønne Græs.
40 Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
Og de satte sig ned, Hob ved Hob, somme paa hundrede og somme paa halvtredsindstyve.
41 Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
Og han tog de fem Brød og de to Fisk, saa op til Himmelen og velsignede; og han brød Brødene og gav sine Disciple dem at lægge for dem, og han delte de to Fisk til dem alle.
42 Dukansu suka ci suka koshi.
Og de spiste alle og bleve mætte.
43 Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
Og de optoge tolv Kurve fulde af Stykker, ogsaa af Fiskene.
44 Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
Og de, som spiste Brødene, vare fem Tusinde Mænd.
45 Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
Og straks nødte han sine Disciple til at gaa om Bord i Skibet og i Forvejen sætte over til hin Side, til Bethsajda, medens han selv lod Skaren gaa bort.
46 Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
Og da han havde taget Afsked med dem, gik han op paa Bjerget for at bede.
47 Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
Og da det var blevet silde, var Skibet midt paa Søen og han alene paa Landjorden.
48 Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
Og da han saa, at de havde deres Nød med at ro (thi Vinden var dem imod), kommer han ved den fjerde Nattevagt til dem vandrende paa Søen. Og han vilde gaa dem forbi.
49 Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
Men da de saa ham vandre paa Søen, mente de, at det var et Spøgelse, og de skrege.
50 gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
Thi de saa ham alle og bleve forfærdede. Men han talte straks med dem og sagde til dem: „Værer frimodige, det er mig, frygter ikke!”
51 Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
Og han steg op i Skibet til dem, og Vinden lagde sig, og de forfærdedes over al Maade ved sig selv.
52 Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
Thi de havde ikke faaet Forstand af det, som var sket med Brødene; men deres Hjerte var forhærdet.
53 Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
Og da de vare farne over til Landet, kom de til Genezareth og lagde til der.
54 Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
Og da de traadte ud af Skibet, kendte man ham straks.
55 Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
Og de løb om i hele den Egn og begyndte at bringe de syge paa deres Senge omkring, hvor de hørte, at han var.
56 Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.
Og hvor som helst han gik ind i Landsbyer eller Byer eller Gaarde, lagde de de syge paa Torvene og bade ham om, at de maatte røre blot ved Fligen af hans Klædebon; og alle de, som rørte ved ham, bleve helbredede.

< Markus 6 >