< Markus 5 >

1 Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa.
Og de kom over på hin side av sjøen, til gerasenernes bygd.
2 Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.
Og da han var gått ut av båten, kom det straks mot ham ut av gravene en mann som var besatt av en uren ånd.
3 Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari
Han hadde sitt tilhold der i gravene, og de kunde ikke lenger binde ham, ikke engang med lenker;
4 An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.
for han hadde ofte vært bundet med fot-jern og lenker, og lenkene hadde han revet av sig, og fot-jernene hadde han sønderslitt, og ingen kunde rå med ham,
5 Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi.
og han var alltid, natt og dag, i gravene og på fjellene og skrek og slo sig selv med stener.
6 Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.
Og da han så Jesus langt borte, løp han til og falt ned for ham,
7 Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala,
og ropte med høi røst: Hvad har jeg med dig å gjøre, Jesus, du den høieste Guds Sønn? Jeg besverger dig ved Gud at du ikke må pine mig!
8 Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa.”
For han sa til ham: Far ut av mannen, du urene ånd!
9 Ya tambaye shi, “Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa.
Og han spurte ham: Hvad er ditt navn? Og han sa til ham: Legion er mitt navn; for vi er mange.
10 Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.
Og han bad ham meget at han ikke måtte drive dem ut av bygden.
11 Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni.
Men det gikk en stor svinehjord og beitet der ved fjellet,
12 Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun.
Og de bad ham: Send oss inn i svinene, så vi kan fare i dem!
13 Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.
Og han gav dem lov til det. Og de urene ånder fór ut og fór i svinene; og hjorden styrtet sig ut over stupet ned i sjøen, omkring to tusen i tallet, og druknet i sjøen.
14 Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru
Og de som gjætte dem, tok flukten, og fortalte det i byen og i bygden. Og folk kom ut for å se hvad som hadde hendt.
15 Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.
Og de kom til Jesus og så den besatte sitte påklædd og ved sans og samling, han som hadde vært besatt av legionen, og de blev forferdet.
16 Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun.
Og de som hadde sett det, fortalte dem hvorledes det var gått med den besatte, og om svinene.
17 Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.
Og de begynte å be ham at han vilde dra bort fra deres landemerker.
18 Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi.
Og da han gikk i båten, bad den besatte om å få være med ham.
19 Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka.
Og han gav ham ikke lov, men sa til ham: Gå hjem til dine og fortell dem hvor store ting Herren har gjort imot dig, og at han har miskunnet sig over dig!
20 Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.
Og han gikk bort og begynte å kunngjøre i Dekapolis hvor store ting Jesus hadde gjort imot ham; og alle undret sig.
21 Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun.
Og da Jesus var faret over med båten til hin side igjen, samlet meget folk sig om ham; og han var ved sjøen.
22 Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa.
Og det kom en av synagoge-forstanderne ved navn Jairus; og da han så ham, falt han ned for hans føtter,
23 Ya yi ta rokonsa, yana cewa, “Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu.”
og han bad ham meget og sa: Min datter ligger på det siste; kom og legg dine hender på henne, så hun må bli frelst og leve!
24 Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.
Og han gikk bort med ham, og meget folk fulgte ham, og de trengte ham.
25 Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu.
Og der var en kvinne som hadde hatt blodsott i tolv år;
26 Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi.
og hun hadde lidt meget av mange læger og satt til alt det hun eide, og hadde ikke hatt nogen hjelp av det, men var heller blitt verre;
27 Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.
da hun hadde hørt ryktet om Jesus, kom hun midt iblandt folket og rørte bakfra ved hans klædebon.
28 Domin ta ce “Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke.”
For hun sa: Kan jeg få røre, om det så bare er ved hans klær, så blir jeg helbredet.
29 Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.
Og straks uttørkedes hennes blods kilde, og hun kjente i sitt legeme at hun var helbredet for sin plage.
30 Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce “wanene ya taba rigata?”
Og Jesus kjente straks hos sig selv den kraft som gikk ut fra ham, og han vendte sig om i hopen og sa: Hvem var det som rørte ved mine klær?
31 Almajiransa suka ce, “a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?”
Og hans disipler sa til ham: Du ser at folket trenger dig på alle kanter, og du sier: Hvem var det som rørte ved mig?
32 Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.
Og han så sig om for å få øie på henne som hadde gjort dette.
33 Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya.
Men kvinnen kom redd og skjelvende, for hun visste hvad som var skjedd med henne, og hun falt ned for ham og sa ham hele sannheten.
34 Sai ya ce da ita, “Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki”.
Da sa han til henne: Datter! din tro har frelst dig; gå bort i fred, og vær helbredet for din plage!
35 Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce “Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?”
Mens han ennu talte, kom det folk fra synagoge-forstanderen og sa: Din datter er død; hvorfor umaker du mesteren lenger?
36 Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, “kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai.”
Men Jesus hørte det ord som blev sagt, og sa til synagoge-forstanderen: Frykt ikke, bare tro!
37 Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu.
Og han lot ingen følge med sig uten Peter og Jakob og Johannes, Jakobs bror.
38 Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.
Og de kom til synagoge-forstanderens hus, og han så en larmende hop og folk i stor gråt og jammer,
39 Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane “Me ya sa kuke damuwa da kuka?” Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi.
og han gikk inn og sa til dem: Hvorfor larmer og gråter I? Barnet er ikke død; hun sover.
40 Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.
Og de lo ham ut. Men han driver alle ut, og tar med sig barnets far og mor og dem som var med ham, og går inn der hvor barnet var.
41 Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita “Tilatha koum” wato yarinya na ce ki tashi”
Og han tar barnet ved hånden og sier til henne: Talita kumi; det er utlagt: Pike! jeg sier dig: Stå op!
42 Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya [gama shekarun ta sun kai goma sha biyu]. Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske.
Og straks stod piken op og gikk omkring; for hun var tolv år gammel. Og de blev storlig forferdet.
43 Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.
Og han bød dem strengt at ikke nogen skulde få dette å vite; og han sa at de skulde gi henne noget å ete.

< Markus 5 >